Fitattun matan da ke takarar majalisar dattawan Najeriya a zaɓen 2027

Asalin hoton, Facebook/FB
Yayin da shirye-shiryen babban zaɓen 2027 ke ƙara ɗaukar hankali a Najeriya, wasu fitattun mata sun shiga fafatawar neman kujerun Majalisar Dattawa a sassa daban-daban na ƙasar.
Matan sun hada da tsofaffin ƴan majalisa da masu riƙe da muƙaman siyasa da kuma wasu da suka yi fice wajen fafutikar siyasa a matakin jiha da ƙasa.
A jerin sunayen ƴan takarar da INEC ta fitar a baya-bayan nan, mata daga manyan jam'iyyu sun bayyana a yankuna daban-daban, lamarin da ke nuna ci gaba da ƙoƙarin ƙara yawan wakilcin mata a siyasar Najeriya.
Sai dai duk da ƙaruwar yawan matan da suka shiga takara a wannan karo, babban ƙalubalen da ya rage musu shi ne shawo kan ƙalubalen da ke gabansu na lashe manyan zaɓukansu.
Aƙalla 22 mata ne suka bayyana a cikin jerin sunayen da INEC ɗin ta wallafa da sunan ƴantakarar majalisar dattawa a 2027.
Ireti Kingibe - Abuja

Asalin hoton, Ireti Kingibe/X
Sanata Kingibe na ɗaya daga cikin fitattun ƴansiyasar Abuja kuma mai riƙe da kujerar Sanatan Babban Birnin Tarayya guda ɗaya tilo a yanzu haka.
Ta yi suna a siyasa bayan nasararta a zaɓen 2023, inda ta zama ɗaya daga cikin mata ƴan majalisar dattawa .
Tuni kuma ta ƙudiri aniyar komawa majalisar a ƙarƙashin jam'iyyar ADC.
Natasha Akpoti-Uduaghan - Kogi

Asalin hoton, Natasha Akpoti-Uduaghan/X
Natasha Akpoti-Uduaghan lauya ce kuma ƴarsiyasa da ta yi fice saboda yadda ta shiga tsakiyar wani ce-ce-ku-ce da shugaban majalisar dattawan ƙasar, Sanata Godswill Akpabio.
Ta shahara a siyasance ne sakamakon fafatawa da ta sha yi kan kujerar Sanata.
Tana daga cikin matan da suka fi jan hankali a siyasar Najeriya a yanzu.
Iyabo Obasanjo – Ogun

Asalin hoton, Iyabo Obasanjo/X
Iyabo Obasanjo ƴar tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ce, kuma ta taɓa zama Sanata mai wakiltar Ogun ta Tsakiya.
Likita ce kuma gogaggiyar ƴar siyasa da aka daɗe da sani a siyasar Najeriya.
Komawarta takarar Sanata a 2027 ya sake jawo hankalin masu bibiyar harkokin siyasa.
Frances Ottah Agbo - Benue
Frances Ottah Agbo ta fito takarar Sanatan Benue ta Kudu a ƙarƙashin APC.
Ta kasance daga cikin fitattun mata da suka samu tikitin jam'iyya a yankin Arewa ta Tsakiya.
Takararta na ƙara fito da mata a sahun gaba na siyasar jihar Benue.
Risikat Motunrayo Abdullahi - Kwara
Risikat Motunrayo Abdullahi ita ce ƴartakarar ADC a Kwara ta Tsakiya.
Tana cikin sabbin fuskokin siyasar jihar Kwara da ke neman wakilci a Majalisar Dattawa.
Nasararta za ta ƙara yawan mata masu wakiltar Arewa ta Tsakiya a majalisar.
Rose Bitrus Mwanti – Plateau

Asalin hoton, Rose Bitrus Mwanti/FB
Rose Bitrus Mwanti tana takarar kujerar Sanatan Plateau ta Arewa a jam'iyyar ADC.
Ta fito daga jihar Plateau inda take neman wakiltar yankin da ke ɗaya daga cikin muhimman yankuna a siyasar jihar.
Takararta na nuna ƙoƙarin mata na shiga fafatawar manyan mukaman siyasa a arewacin Najeriya.
Rabi Aliyu - Kano
Rabi Aliyu na daga cikin matan da suka tsunduma siyasar Kano, jihar da yawan mata masu neman manyan kujeru ba su da yawa.
Ta fito takara a ƙarƙashin jam'iyyar AAC, tana neman wakiltar Kano ta Tsakiya.
Shigarta takara na ƙara faɗaɗa zaɓin masu kaɗa ƙuri'a a yankin.
Jamila Muhammed – Kano
Jamila Muhammed tana cikin matan da ke son samun gurbi a Majalisar Dattawa ita ma daga jihar Kano.
Ta fito ne a ƙarƙashin jam'iyyar NDP, tana neman nuna cewa mata ma na iya taka rawa a manyan kujerun siyasa.
Takararta na zuwa ne a lokacin da ake kira da a ƙara bai wa mata dama a siyasar Najeriya.
Idiat Oluranti Adebule - Lagos
Idiat Oluranti Adebule tsohuwar mataimakiyar gwamnan jihar Legas ce kuma Sanata mai wakiltar Lagos ta Yamma.
Malama ce kuma gogaggiyar ƴarsiyasa da ta daɗe tana riƙe manyan muƙamai a gwamnati.
A zaɓen 2027 tana neman takarar Majalisar Dattawa a ƙarƙashin APC.











