Fitattun matan da ke takarar majalisar dattawan Najeriya a zaɓen 2027

Mata

Asalin hoton, Facebook/FB

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 4

Yayin da shirye-shiryen babban zaɓen 2027 ke ƙara ɗaukar hankali a Najeriya, wasu fitattun mata sun shiga fafatawar neman kujerun Majalisar Dattawa a sassa daban-daban na ƙasar.

Matan sun hada da tsofaffin ƴan majalisa da masu riƙe da muƙaman siyasa da kuma wasu da suka yi fice wajen fafutikar siyasa a matakin jiha da ƙasa.

A jerin sunayen ƴan takarar da INEC ta fitar a baya-bayan nan, mata daga manyan jam'iyyu sun bayyana a yankuna daban-daban, lamarin da ke nuna ci gaba da ƙoƙarin ƙara yawan wakilcin mata a siyasar Najeriya.

Sai dai duk da ƙaruwar yawan matan da suka shiga takara a wannan karo, babban ƙalubalen da ya rage musu shi ne shawo kan ƙalubalen da ke gabansu na lashe manyan zaɓukansu.

Aƙalla 22 mata ne suka bayyana a cikin jerin sunayen da INEC ɗin ta wallafa da sunan ƴantakarar majalisar dattawa a 2027.

Ireti Kingibe - Abuja

Ireti Kingibe

Asalin hoton, Ireti Kingibe/X

Sanata Kingibe na ɗaya daga cikin fitattun ƴansiyasar Abuja kuma mai riƙe da kujerar Sanatan Babban Birnin Tarayya guda ɗaya tilo a yanzu haka.

Ta yi suna a siyasa bayan nasararta a zaɓen 2023, inda ta zama ɗaya daga cikin mata ƴan majalisar dattawa .

Tuni kuma ta ƙudiri aniyar komawa majalisar a ƙarƙashin jam'iyyar ADC.

Natasha Akpoti-Uduaghan - Kogi

Natasha Akpoti-Uduaghan

Asalin hoton, Natasha Akpoti-Uduaghan/X

Natasha Akpoti-Uduaghan lauya ce kuma ƴarsiyasa da ta yi fice saboda yadda ta shiga tsakiyar wani ce-ce-ku-ce da shugaban majalisar dattawan ƙasar, Sanata Godswill Akpabio.

Ta shahara a siyasance ne sakamakon fafatawa da ta sha yi kan kujerar Sanata.

Tana daga cikin matan da suka fi jan hankali a siyasar Najeriya a yanzu.

Iyabo Obasanjo – Ogun

Iyabo Obasanjo

Asalin hoton, Iyabo Obasanjo/X

Iyabo Obasanjo ƴar tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ce, kuma ta taɓa zama Sanata mai wakiltar Ogun ta Tsakiya.

Likita ce kuma gogaggiyar ƴar siyasa da aka daɗe da sani a siyasar Najeriya.

Komawarta takarar Sanata a 2027 ya sake jawo hankalin masu bibiyar harkokin siyasa.

Frances Ottah Agbo - Benue

Frances Ottah Agbo ta fito takarar Sanatan Benue ta Kudu a ƙarƙashin APC.

Ta kasance daga cikin fitattun mata da suka samu tikitin jam'iyya a yankin Arewa ta Tsakiya.

Takararta na ƙara fito da mata a sahun gaba na siyasar jihar Benue.

Risikat Motunrayo Abdullahi - Kwara

Risikat Motunrayo Abdullahi ita ce ƴartakarar ADC a Kwara ta Tsakiya.

Tana cikin sabbin fuskokin siyasar jihar Kwara da ke neman wakilci a Majalisar Dattawa.

Nasararta za ta ƙara yawan mata masu wakiltar Arewa ta Tsakiya a majalisar.

Rose Bitrus Mwanti – Plateau

Rose Bitrus Mwanti

Asalin hoton, Rose Bitrus Mwanti/FB

Rose Bitrus Mwanti tana takarar kujerar Sanatan Plateau ta Arewa a jam'iyyar ADC.

Ta fito daga jihar Plateau inda take neman wakiltar yankin da ke ɗaya daga cikin muhimman yankuna a siyasar jihar.

Takararta na nuna ƙoƙarin mata na shiga fafatawar manyan mukaman siyasa a arewacin Najeriya.

Rabi Aliyu - Kano

Rabi Aliyu na daga cikin matan da suka tsunduma siyasar Kano, jihar da yawan mata masu neman manyan kujeru ba su da yawa.

Ta fito takara a ƙarƙashin jam'iyyar AAC, tana neman wakiltar Kano ta Tsakiya.

Shigarta takara na ƙara faɗaɗa zaɓin masu kaɗa ƙuri'a a yankin.

Jamila Muhammed – Kano

Jamila Muhammed tana cikin matan da ke son samun gurbi a Majalisar Dattawa ita ma daga jihar Kano.

Ta fito ne a ƙarƙashin jam'iyyar NDP, tana neman nuna cewa mata ma na iya taka rawa a manyan kujerun siyasa.

Takararta na zuwa ne a lokacin da ake kira da a ƙara bai wa mata dama a siyasar Najeriya.

Idiat Oluranti Adebule - Lagos

Idiat Oluranti Adebule tsohuwar mataimakiyar gwamnan jihar Legas ce kuma Sanata mai wakiltar Lagos ta Yamma.

Malama ce kuma gogaggiyar ƴarsiyasa da ta daɗe tana riƙe manyan muƙamai a gwamnati.

A zaɓen 2027 tana neman takarar Majalisar Dattawa a ƙarƙashin APC.