KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Asabar 19/09/2026

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Aisha Aliyu Ja'afar
  • Tsadar farashin mai
  • Yadda sheikh Lukuwa
  • Hoto
  • Cyber Truck
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Waɗanda suka mutu a harin Masallaci a Pakistan sun haura 30

    Pakistan

    Asalin hoton, Reuters

    Adadin mutanen da suka mutu a harin bam da aka kai da mota a wata masallaci a arewa maso yammacin Pakistan ranar Juma’a ya haura 30, kamar yadda rahotanni suka nuna.

    Jami’ai sun ce an tayar da wata mota da aka cika da abubuwan fashewa a gaban masallacin da ke gundumar Kohat a lardin Khyber Pakhtunkhwa, kafin wasu ‘yan bindiga su kutsa cikin wani sansanin ‘yan sanda da ke makwabtaka da masallacin.

    Fiye da mutum 100 sun jikkata.

    Jami’an tsaro sun ce yanzu an kammala share gine-ginen bayan wani samame da suka kwashe dare suna gudanarwa.

    Pakistan ta fuskanci karuwar hare-haren ta’addanci sosai tun bayan da Taliban ta sake dawo da iko a Afghanistan da ke makwabtaka da kasar.

  2. Amurka ta sake lafta wa Rasha takunkumi

    Amurka da Rasha

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaba Trump ya rattaba hannu kan kudirin dokar ƙaƙaba sabbin takunkumai masu tsauri kan Rasha, bayan da Majalisar Wakilai ta amince da kudurin da gagarumin rinjaye a ranar Laraba.

    Wakilin BBC ya ce magoya baya dai sun ce makasudin dokar shi ne dakile kudaden shiga da Rasha ke samu daga man fetur da iskar Gas da ta ke amfani da su wurin gudanar da yakinta kan Ukraine.

    Dokar za ta bai wa Shugaban Trump damar sanya harajin kasuwanci mai nauyi, idan ya ga dama, kan manyan kasashe masu sayen man fetur da iskar gas daga Moscow, kamar su China da Indiya.

  3. Trump ya hana CNN shiga fadar White House domin ɗauko labarai

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Trump ya ce zai hana wasu manyan kafofin yada labarai na Amurka guda uku shiga Fadar White House nan take.

    A wani sako da ya wallafa a shafukan sada zumunta, ya zargi CNN da MS Now da Politico da ci gaba da yada "labaran karya," inda ya ce wannan matakin hana shiga martani ne kan hakan.

    Wakiliyar BBC ta ce A baya shugaba Trump Ya dauki matakin shari'a kan wasu kafofin yada labarai da suka hada da New York Times da BBC, kuma akai-akai yana samun sabani tare da cin mutuncin yan jarida.

    A cikin wata sanarwa, CNN ta bayyana matakin a matsayin cin zarafi da ya saba wa doka, tare da take hakkinsu na gudanar da aiki ba tare da cikas ko tsangwama daga gwamnati ba.

  4. Buɗewa

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Asabar daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu kawo muku labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ma sassan duniya.

    Ku leƙa shafukanmu na sada zumunta domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo da kuma yin muhawara.

    Ku kasance tare da mu.