Waɗanda suka mutu a harin Masallaci a Pakistan sun haura 30

Asalin hoton, Reuters
Adadin mutanen da suka mutu a harin bam da aka kai da mota a wata masallaci a arewa maso yammacin Pakistan ranar Juma’a ya haura 30, kamar yadda rahotanni suka nuna.
Jami’ai sun ce an tayar da wata mota da aka cika da abubuwan fashewa a gaban masallacin da ke gundumar Kohat a lardin Khyber Pakhtunkhwa, kafin wasu ‘yan bindiga su kutsa cikin wani sansanin ‘yan sanda da ke makwabtaka da masallacin.
Fiye da mutum 100 sun jikkata.
Jami’an tsaro sun ce yanzu an kammala share gine-ginen bayan wani samame da suka kwashe dare suna gudanarwa.
Pakistan ta fuskanci karuwar hare-haren ta’addanci sosai tun bayan da Taliban ta sake dawo da iko a Afghanistan da ke makwabtaka da kasar.




















