Jami'an Afirka ta Kudu na binciken kisan 'yan Najeriya biyu a ƙasar

Asalin hoton, EPA
Hukumar sa ido kan ayyukan 'yansanda ta Afirka ta Kudu IPID ta tabbatar da cewa tana binciken wani ƙorafi da aka shigar kan jami'an 'yan sanda a birnin Pretoria bayan mutuwar wasu ƴan Najeriya.
Hukumar ta ce an shigar da ƙorafin ne a makon da ya gabata, amma ta ce har yanzu ba za ta iya bayyana cikakkun bayanai kan lamarin ba yayin da bincike ke gudana.
Rahotanni sun nuna cewa ɗaya ya mutu ne yayin wata takaddama da ta shiga tsakaninsa da jami'an 'yansanda.
A ranar 28 ga Yuni a lardin Mpumalanga kuma 'yansanda sun tabbatar da cewa suna binciken kisan ɗayan, wanda shi mai gidan gyaran gashi ne da aka harbe a wajen shagonsa da ke garin eMalahleni, tsohon Witbank.
A cewar 'yansanda, wani mutum dauke da makami ne ya tare shi sannan ya harbe shi har lahira kafin ya tsere cikin wata farar mota.
Har yanzu ba a kama kowa ba, kuma ba a san dalilin kashe ƴn Najeriya ɗin ba.
'Yansandan suna kira ga duk wanda ke da bayanin da zai taimaka wajen cafke wanda ake zargi da ya tuntuɓe su.




























