'A yi taka-tsantsan kan hukuncin kotu game da asalin ɗanƙasa a Filato'

Asalin hoton, Caleb Mutfwang/X
Gwamnatin Filato ta yi kira ga al'ummar jihar da su yi taka-tsantsan da kauce wa kalamai ko ɗaukar matakan da za su iya tayar da hankali bayan hukuncin da kotu ta yanke kan batun bayar da takardun shaidar asalin ɗan ƙasa a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.
A cikin wata sanarwa da kwamishinar yaɗa labarai ta jihar, Joyce Lohya Ramnap, ta fitar, gwamnatin ta bayyana damuwarta kan yadda batun "ya haifar da muhawara mai zafi da ka iya haifar da rashin jituwa tsakanin al'ummomin da suka shafe shekaru suna zaman lafiya tare".
Wata Bahaushiya mai suna Fatima Akawu da aka haifa kuma ta tashi a Jos ce ta shigar da ƙaramar hukumar Jos ta Arewa ƙara bayan da ta buƙaci shaidar zama ƴar Jos ta Arewa aka hana, inda aka aka ba ta takardar shaidar ɗan ƙasa ta wucin-gadi.
Babbar kotun jihar ta umurci ƙaramar hukumar ta ba ta cikakkiyar takardar shaidar zama ɗan ƙasa (Indigene) cikin kwana 30, inda ta yanke hukuncin cewa "duk wanda aka haifa kuma ya tashi a ƙaramar hukumar yana da haƙƙin samun shaidar".
Gwamnatin ta bayyana cewa ƙaramar hukumar Jos ta Arewa, ba ta gamsu da hukuncin kotun ba, inda ta ce tana da haƙƙin ɗaukaka ƙara a kotu ta gaba, bisa tanadin doka.
"Duk da cewa gwamnati tana girmama haƙƙin ƴan ƙasa na bayyana ra'ayoyinsu kan al'amuran da suka shafi jama'a, tana kira ga kowa da kowa da ya nuna dattaku, sanin ya kamata da taka-tsantsan wajen yin tsokaci kan wannan batu," in ji sanarwar.
Haka kuma gwamnatin ta bayyana cewa ba za ta goyi bayan duk wani yunƙuri na amfani da lamarin wajen haifar da ƙiyayya, rarrabuwar kai ko tayar da fitina tsakanin al'ummomi ba. Ta jaddada aniyarta na ci gaba da kare doka, mutunta 'yancin shari'a da samar da yanayin da kowa zai gudanar da harkokinsa cikin lumana.
Sai dai gwamnatin ta ce, bai dace a taƙaita irin wannan hukunci ga ƙaramar hukumar Jos ta Arewa kaɗai ba.




























