Iran na ƙarfafa hulɗa da Saudiyya da Pakistan kafin tattaunawarta da Amurka

Asalin hoton, IRNA
Iran na ci gaba da ƙarfafa hulɗarta da Saudiyya da Pakistan ta hanyar tattaunawa da manyan jami'an ƙasashen biyu, a daidai lokacin da ake sa ran fara sabon zagayen tattaunawa tsakanin Tehran da Washington cikin sa'o'i masu zuwa.
Kamfanin dillancin labaran gwamnatin Iran (IRNA) ya ruwaito cewa ministan harkokin wajen ƙasar, Abbas Araqchi, ya yi tattaunawa ta biyu a ranar Lahadi da takwaransa na Saudiyya, Faisal bin Farhan Al Saud.
Haka kuma ya yi wata tattaunawa ta wayar tarho da ministan harkokin wajen Pakistan, sannan daga bisani ya tuntubi shugaban rundunar sojin Pakistan, Field Marshal Asim Munir, wanda ake kallon sa a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu tasiri a harkokin tsaro da siyasar ƙasar.
Wadannan tattaunawa na zuwa ne bayan shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa za a fara sabon zagayen tattaunawa tsakanin Amurka da Iran, inda za a mayar da hankali kan batutuwan mashigin ruwa na Hormuz da kuma shirin nukiliyar Iran.
















