Venezuela za ta kafa sansanonin wucin-gadi ga waɗanda girgizar ƙasa ta shafa

Asalin hoton, Getty Images
Shugabar riƙon ƙwarya ta Venezuela, Delcy Rodríguez, ta ce gwamnati za ta kafa sansanonin wucin-gadi domin ba da mafaka ga mutanen da gidajensu suka lalace sakamakon girgizar ƙasar da ta afku a makon da ya gabata.
Ta ce kwamitin da aka kafa zai dinga tantance lafiyar gine-gine ta amfani da tsarin launukan ja, da kore da rawaya.
Yawan waɗanda suka mutu ya haura 1,700, yayin da har yanzu ba a san inda dubban mutane suke ba.
Har yanzu jami'an ceto na ci gaba da zaƙulo mutane da rai daga ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine, duk da cewa kwanaki biyar sun shige tun bayan afkuwar tagwayen girgizar ƙasar.
Sai dai wakilin BBC a birnin La Guaira, wanda shi ne yankin da lamarin ya fi muni, ya ce aikin ceton na fuskantar ƙalubale, har ta kai ga sojoji na neman shawara daga fararen hula kan hanyoyin da suka fi dacewa wajen taimakawa.
Wakilin ya kuma ce ƴan Venezuela na ci gaba da tururuwar zuwa yankunan da girgizar kasar ta shafa domin bayar da gudummawarsu.



































