Sojojin Myanmar sun kashe fararen hula 700 cikin wata shida, in ji MDD

Asalin hoton, Getty Images
Sojojin Myanmar ne ke da alhakin kashe fararen hula fiye da 700 a cikin wata shidan da ke kewaye da lokacin zaben shekarar da ta gabata, in ji MDD.
Wani sabon rahoto da aka haɗa daga watan Agusta zuwa Janairu ya ce sahihan majiyoyi sun tabbatar da kashe aƙalla mutum 702 da suka haɗa da mata 224 da ƙananan yara 153.
Ya shafi watanni shida ne daga lokacin da sojoji - waɗanda suka yi juyin mulki shekara biyar da suka wuce - suka sanar da gudanar zabuka, tsarin da ake yi wa kallon na jeka na yi ka ne saboda an cire manyan jam'iyyun adawa.
Rahoton ya yi gargaɗin "raguwar tallafin ƙasa da ƙasa na kara wahalhalun da miliyoyin mutane ke fuskanta".
Sojojin Myanmar sun ƙaddamar da juyin mulkin ne a shekarar 2021, wanda ya haifar da yaƙin basasa inda aka kashe dubban mutane tare da raba miliyoyi da muhallansu.
Manyan yankunan ƙasar na ci gaba da kasancewa ƙarƙashin ikon ƙungiyoyin ƴan adawa masu ɗauke da makamai.































