KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 12/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 12 ga watan Yulin 2026.

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammad

  1. Iran ta harba mana makaimai masu linzami uku - Jordan

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Sojojin Jordan sun sanar da cewa makamai masu linzami uku da aka harba daga Iran sun faɗo a wasu sassan ƙasar da safiyar Lahadi.

    A cikin wata sanarwa, wata majiya ta soja ta ce makaman sun sauka ne a wurare daban-daban na masarautar Jordan, amma babu wanda ya rasa ransa ko ya jikkata sakamakon lamarin.

    Majiyar ta ƙara da cewa ɓarnar da aka samu ta takaita ne ga ƙananan lalacewar kadarori kaɗai.

  2. Iran da Oman sun tattauna kan gudanar da zirga-zirgar Jirage a mashigar Hormuz

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce tattaunawar da ministan harkokin wajen ƙasar Abbas Araqchi ya yi da jami'an Oman a Muscat ta mayar da hankali ne kan yadda za a gudanar da zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz.

    Baghaei ya bayyana cewa tawagogin ƙwararru na fannin shari'a da fasaha daga ƙasashen biyu sun halarci tattaunawar, inda suka yi musayar ra'ayi kan tabbatar da tsaro da lafiyar zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar.

    Ya ce an tattauna batutuwan da suka shafi mutunta 'yancin mallaka na ƙasashen biyu da ke gaɓar mashigar, da kuma bin dokokin ƙasa da ƙasa, tare da tanade-tanaden sashe na biyar na Yarjejeniyar Fahimtar Juna ta Islamabad.

    Baghaei ya ƙara da cewa Iran ta jaddada cewa duk wani sabon tsari na gudanar da zirga-zirga a mashigar Hormuz ya kamata ya kasance sakamakon shawarwari tsakanin Iran da Oman.

  3. Tsohon sarkin Qatar Sheikh Hamad bin Khalifa Al Thani ya rasu

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Gwamnatin Qatar ta sanar da rasuwar tsohon sarkin ƙasar, Sheikh Hamad bin Khalifa Al Thani, yana da shekaru 74 a duniya.

    Sheikh Hamad ya jagoranci harkokin mulkin Qatar daga shekarar 1995 zuwa 2013, kuma ana kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu gina Qatar ta zamani.

    A lokacin mulkinsa, ƙasar ta samu gagarumin ci gaban tattalin arziki, wanda ya taimaka wajen ɗaga darajar Qatar a idon duniya.

    Haka kuma, a shekarar 1996 ne aka ƙaddamar da tashar talabijin ta Al Jazeera bisa umarninsa, lamarin da ya sanya kafar yada labaran ta zama ɗaya daga cikin shahararrun kafofin watsa labarai a duniya.

    Rasuwarsa ta jawo alhini a Qatar da ma sauran sassan duniya, inda ake tuna irin rawar da ya taka wajen sauya fasalin ƙasar.

  4. Iran ta sanar da kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka biyar a yankin Gabas ta Tsakiya

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta ce ta kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka guda biyar da ke Oman, Jordan, Kuwait, Bahrain da Qatar, a wani mataki da ta bayyana a matsayin martani ga hare-haren da Amurka ke kai wa yankunan kudancin ƙasar.

    A cikin wata sanarwa, rundunar juyin juya halin Iran ta ce rundunar sararin samaniyarta ta kai hari kan cibiyoyin kayan aikin jiragen ruwa masu ɗaukar jiragen yaƙin Amurka da kuma wuraren man fetur a tashar jiragen ruwa ta Duqm da ke Oman.

    IRGC ta kuma bayyana cewa ta yi amfani da makamai masu linzami wajen kai harin kan muhimman cibiyoyin soja da kayayyakin more rayuwa a sansanin sojin sama na Prince Hassan da ke Jordan.

    Iran ta ce hare-haren wani ɓangare ne na martanin da take mayarwa kan abin da ta zargi Amurka da aikatawa na "cin zarafin soja", yayin da ake ci gaba da samun tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Har yanzu dai babu wata sanarwa daga hukumomin Amurka, Kuwait, Bahrain ko Qatar kan waɗannan iƙirare.

  5. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,barkanmu da wannan safiya ta ranar Lahadi.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.