APC ta tabbatar da Abba, Radda da Dauda ƴantakarar gwamna
Jam’iyyar APC ta tabbatar da gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf a matsayin ɗan takararta na maslaha domin shiga zaɓen 2027.
Jam'iyyar ta zabi gwamna Abba a yayin taron amincewa da ya gudana a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata a yau Alhamis.

Asalin hoton, Abba Kabir Yusuf/FB
A jihar Zamfara ma, gwamna Dauda Lawal da ke neman wa'adi na biyu ya samu tikitin takarar a jam’iyyar APC.
An tabbatar da gwamna Dauda a matsayin dan takarar APC ba tare da hamayya ba.

Asalin hoton, Dauda Lawal
Shi ma gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya lashe tikitin takarar gwamna na jam’iyyar domin neman wa’adi na biyu.
Ya samu nasarar ne bayan zama ɗan takara tilo na jam’iyyar ta hanyar amincewar bai-ɗaya daga wakilan dukkan mazaɓu 225 da ke faɗin jihar.

Asalin hoton, Nasir Idris/FB
Gwamna Dikko Radda na jihar Katsina ma ya samu tikitin a yayin wani taro da aka gudanar domin tabbatar da shi a yau Alhamis.

Asalin hoton, Hannatu Musawa/FB
Gwamna Ahmad Aliyu na Sokoto ma ya samu tikitinsa na takarar a karo na biyu bayan da magoya bayan jam'iyyar ta amince da shi.

Asalin hoton, Sokoto Govt
Jam'iyar APCn ta ɗage zaɓen a jihohin Bauchi da Kwara, inda ake jiran jihohin Adamawa, Jigawa, Yobe, Niger, Taraba, Filato da Borno a yankin Arewacin Najeriya, duk da yake yawancinsu an cimma masalaha.
A jihar Kaduna kuwa an amince da Uba Sani a matsayin dantakarar, sai kuma Jamilu Isiyaku Gwamna a jihar Gombe.
Mataimakin gwamnan jihar Legas Obafemi Hamzat ne aka tabbatar a matsayin ɗantakarar gwamnan jihar.

























