Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Asabar 19/09/2026

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Abin da ya sa muke goyon bayan Tinubu ya zarce - Rarara

    Mawaƙin siyasa a Najeriya, Dauda Kahutu Rarara ya ce shi da sauran ƴan Kanywood na goyon bayan Shugaba Tinubu saboda "ba ya ƙarya da yaudara".

    Rarara ya kuma nemi ƴan ƙasar su yi haƙuri da yanayin da ake ciki.

  2. Zelensky ya yaba wa Trump bisa amincewa da takunkumi kan Iran da Rasha

    A baya mun ruwaito cewa Donald Trump ya rattaba hannu kan wata doka da ta kakaba tsauraran takunkumi kan Rasha tare da tsawaita takunkuman da aka kakaba wa Iran.

    Yanzu Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya gode wa shugaban Amurka kan rattaba hannu kan dokar.

    Sanata Lindsey Graham na jam’iyyar Republican ne ya taimaka wajen rubuta dokar, wanda ya rasu a farkon wannan bazarar. Kafin rasuwarsa, Mista Graham ya kai ziyara Ukraine.

    Mista Zelensky ya rubuta a shafin sada zumunta na X cewa: “Hanya mafi kyau ta girmama ƙwaƙwalwar Lindsay ita ce a aiwatar da tanade-tanaden wannan doka gaba ɗaya kuma cikin gaggawa.”

  3. Waɗanda suka mutu a harin Masallaci a Pakistan sun haura 30

    Adadin mutanen da suka mutu a harin bam da aka kai da mota a wata masallaci a arewa maso yammacin Pakistan ranar Juma’a ya haura 30, kamar yadda rahotanni suka nuna.

    Jami’ai sun ce an tayar da wata mota da aka cika da abubuwan fashewa a gaban masallacin da ke gundumar Kohat a lardin Khyber Pakhtunkhwa, kafin wasu ‘yan bindiga su kutsa cikin wani sansanin ‘yan sanda da ke makwabtaka da masallacin.

    Fiye da mutum 100 sun jikkata.

    Jami’an tsaro sun ce yanzu an kammala share gine-ginen bayan wani samame da suka kwashe dare suna gudanarwa.

    Pakistan ta fuskanci karuwar hare-haren ta’addanci sosai tun bayan da Taliban ta sake dawo da iko a Afghanistan da ke makwabtaka da kasar.

  4. Amurka ta sake lafta wa Rasha takunkumi

    Shugaba Trump ya rattaba hannu kan kudirin dokar ƙaƙaba sabbin takunkumai masu tsauri kan Rasha, bayan da Majalisar Wakilai ta amince da kudurin da gagarumin rinjaye a ranar Laraba.

    Wakilin BBC ya ce magoya baya dai sun ce makasudin dokar shi ne dakile kudaden shiga da Rasha ke samu daga man fetur da iskar Gas da ta ke amfani da su wurin gudanar da yakinta kan Ukraine.

    Dokar za ta bai wa Shugaban Trump damar sanya harajin kasuwanci mai nauyi, idan ya ga dama, kan manyan kasashe masu sayen man fetur da iskar gas daga Moscow, kamar su China da Indiya.

  5. Trump ya hana CNN shiga fadar White House domin ɗauko labarai

    Shugaba Trump ya ce zai hana wasu manyan kafofin yada labarai na Amurka guda uku shiga Fadar White House nan take.

    A wani sako da ya wallafa a shafukan sada zumunta, ya zargi CNN da MS Now da Politico da ci gaba da yada "labaran karya," inda ya ce wannan matakin hana shiga martani ne kan hakan.

    Wakiliyar BBC ta ce A baya shugaba Trump Ya dauki matakin shari'a kan wasu kafofin yada labarai da suka hada da New York Times da BBC, kuma akai-akai yana samun sabani tare da cin mutuncin yan jarida.

    A cikin wata sanarwa, CNN ta bayyana matakin a matsayin cin zarafi da ya saba wa doka, tare da take hakkinsu na gudanar da aiki ba tare da cikas ko tsangwama daga gwamnati ba.

  6. Buɗewa

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Asabar daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu kawo muku labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ma sassan duniya.

    Ku leƙa shafukanmu na sada zumunta domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo da kuma yin muhawara.

    Ku kasance tare da mu.