Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 30 ga watan Yulin 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed da Abdullahi Bello

  1. Ƙungiyar likitoci a Najeriya ta yi barazanar shiga yajin aiki

    Ƙungiyar likitocin horaswa ta yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa a Najeriya (NARD) ta yi barazanar shiga yajin aiki na sai baba-ta-gani idan har gwamnatin tarayya ba ta biya buƙatunta ba.

    NARD ta ce za ta tsunduma yajin aikin ne a ranar 10 ga watan Agusta saboda gaza biyan buƙatunta da suka shafi bashin albashi da inganta walwalarsu da kuma yanayin aiki ba.

    Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, ƙungiyar ta cimma wannan matsaya ne a ƙarshen taron Kwamitin zartarwarta da aka gudanar a Gombe daga ranar 26 zuwa 31 ga watan Yuli.

    A yayin taron ne wakilan ƙungiyar suka duba yadda aka aiwatar da yarjejeniyoyin da aka cimma da gwamnatin tarayya a baya, tare da nazarin matsalolin da ke addabar fannin lafiya a ƙasar.

    Shugaban NARD, Dakta Mohammad Usman Suleiman, ya ce ƙungiyar ta nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnatin ke tafiyar hawainiya wajen cika alƙawuran da aka yi, duk da tattaunawa da aka shafe watanni ana yi.

    Ya ce ƙungiyar ta tsawaita wa'adin yajin aikin har sau huɗu domin bai wa gwamnati damar warware matsalolin, amma ya ce har yanzu yawancin alƙawuran ba a cika su ba.

  2. Ba ma so a riƙa amfani da sojoji a lokacin zaɓe - INEC

    Farfesa Joash Amupitan

    Asalin hoton, INEC

    Hukumar zaɓe ta Najeriya, INEC ta ce ba ta goyon bayan a riƙa tura sojoji domin aikin tsaro a lokacin zaɓe

    INEC ta ce ya kamata a riƙa amfani da sojoji ne kawai a lokutan da yanayin tsaro ya zama tilas ba wai a maida hakann al'ada ba.

    Daily Trust ta ruwaito cewa shugaban hukumar, Farfesa Joash Amupitan, ne ya bayyana hakan ta bakin Daraktan Sashen Shari'a na INEC, Al-Hassan Umar, yayin da yake gabatar da jawabi a wani taron karawa juna sani da aka gudanar a Kwalejin Yaƙi ta Sojoji da ke Abuja.

    Ya ce kundin tsarin mulkin Najeriya ya INEC ce ke da alhakin shiryawa, gudanarwa da kuma sa ido kan zaɓe.

    Ya kuma ce rundunar ƴan sandan Najeriya ita ce hukuma ta farko da ke da alhakin tabbatar da tsaro a lokacin zaɓe

    "Rawar da rundunar soji ke takawa ta musamman ce. Ana tura dakarun soji ne kawai idan halin tsaro ya yi muni domin su taimaka wa sauran hukumomi, kuma hakan yake a kundin tsarin mulki," in ji shi.

  3. Amurka ta ƙaryata iƙirarin Iran na lalata jiragen yaƙinta

    Jiragen yaƙin Amurka

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar Sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya (CENTCOM) ta musanta iƙirarin da dakarun juyin juya halin Iran (IRGC) suka yi cewa sun lalata wasu jiragen yaƙin Amurka a hare-haren baya-bayan nan.

    CENTCOM ta bayyana iƙirarin a matsayin ƙarya tsagwaronta, inda ta ce babu wani jirgin yaƙin Amurka, ciki har da jiragen F-35, da ya lalace ko aka lalata.

    Ta kuma ce an yi nasarar kakkaɓo dukkan makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi da Iran ta harba, ko kuma ba su kai ga wuraren da aka nufa ba.

    Rundunar ta kuma yi watsi da iƙirarin IRGC cewa hanyoyin zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz ba su da tsaro, kuma babban abin da ke barazana ga jiragen dakon kaya shi ne hare-haren da IRGC ke kai wa.

  4. Qatar ta yi Allah wadai da hare-haren Iran kan Jordan da Kuwait

    Qatar ta yi Allah wadai da sabbin hare-haren da Iran ta kai kan Jordan da Kuwait, inda ta bayyana su a matsayin take haƙƙin ikon ƙasashen biyu da kuma keta dokokin ƙasa da ƙasa na Majalisar Ɗinkin Duniya.

    A cikin wata sanarwa da Ma'aikatar Harkokin Wajen Qatar ta fitar, ta yi gargaɗin cewa hare-haren na iya ƙara rura wutar rikici a yankin tare da kawo cikas ga ƙoƙarin diflomasiyya na shawo kan rikicin yankin.

    Qatar ta kuma yi kira da a dakatar da duk wani matakin soja cikin gaggawa, tare da komawa kan teburin tattaunawa da sulhu.

  5. Mun kashe ƴanbindiga uku tare da ceto mutum tara da aka yi garkuwa da su - Sojojin Najeriya

    Tsaro

    Asalin hoton, @DefenseNigeria

    Jami'an tsaron Najeriya sun kashe wasu mutum uku da ake zargin 'yan bindiga ne, tare da ceto mutum tara da aka yi garkuwa da su a wani samame da suka kai a jihar Kwara, kamar yadda shafin Channels Television mai zaman kansa ya ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

    An gudanar da samamen ne tare da haɗin gwiwar jami'an Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), dakarun tsaron gandun daji da mafarauta da kuma 'yan sa-kai a yankunan Obbo-Aiyegunle, Ejiu-Ora da Osi da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara, kusa da iyakar jihar Neja.

    An yi garkuwa da mutanen ne daga al'ummar Eju, kuma ana cikin tafiya da su ta cikin daji zuwa jihar Neja lokacin da jami'an tsaron suka kai dauki.

    Jihar Kwara ta fuskanci ƙaruwa a hare-haren da ake kai wa fararen hula da jami'an tsaro cikin watannin baya-bayan nan.

    A ranar 22 ga Yuli, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da kafa sabon bataliyar sojoji a jihar domin yaƙar masu aikata laifuka, ciki har da 'yan bindiga da kuma ƙungiyar Mahmuda, wadda gwamnati ta bayyana a matsayin wani reshe na Boko Haram.

  6. Alƙali ya sha da ƙyar bayan harin ƴanbindiga a kotu a Katsina

    Alkali

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu ƴanbindiga sun kai hari a wata kotun shari'a da ke jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya a ranar 29 ga Yuli, inda alƙalin kotun ya tsere kafin maharan su kutsa, kamar yadda Daily Trust mai zaman kanta ta ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

    Mazauna yankin sun ce Alƙali Mohammed Muktar ya tsere ta taga bayan ya hango maharan na tunkarar kotun da ke ƙauyen Gwarjo a ƙaramar hukumar Matazu.

    Wani mazaunin yankin ya ce: "Ƴanbindigar sun shiga cikin kotun suna harbe-harben kan mai uwa da wabi, kuma suna ta tambayar inda alƙalin yake. Amma sai ya samu nasarar tserewa ta taga, sannan wani ɗan acaba ya taimaka masa kafin su iso."

    Wani ganau ya kuma ce maharan sun yi barazanar kashe Alƙali Muktar idan har ya sake dkomawa domin sauraron shari'o'i.

    Mazauna yankin na ganin cewa 'yan bindigar sun zo ne domin kashe alƙalin ko kuma su yi garkuwa da shi domin neman kuɗin fansa.

  7. MDD ta tsawaita takunkumai kan ƙungiyoyin ƴanbindiga a Afirka ta Tsakiya

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta tsawaita takunkumi kan ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta tsawaita takunkumin da ta ƙaƙabawa ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai da kuma mutanen da ake zargi da kawo cikas ga ƙoƙarin samar da zaman lafiya a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, yayin da rikici ke ci gaba da ta'azzara a ƙasar.

    A ƙuri'ar da Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya ya kaɗa a ranar Laraba, an amince da ƙudurin da ya wajabta wa ƙasashe mambobi su ɗauki matakan hana kai ko sayar da makamai da sauran kayan yaƙi ga ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.

    Takunkumin, wanda aka tsawaita har zuwa 31 ga Yulin 2027, ya kuma haɗa da haramta wa waɗanda abin ya shafa yin tafiye-tafiye da kuma ƙwace kadarorinsu.

    Da yake jawabi a zaman, wakilin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya a Majalisar Ɗinkin Duniya, Marius Aristide Hoja Nzessioué, ya yi maraba da tsawaita takunkumin.

    Sai dai ya kuma yi kira ga ƙasashe da su tabbatar da bin matakan takunkumin yadda ya kamata, yana mai nuna takaicinsa cewa har yanzu 'yan tawaye na samun makamai duk da waɗannan matakan.

    A lokacin da rikicin cikin gida ya ɓarke a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya a shekarar 2013, Majalisar Ɗinkin Duniya ta kakaba wa ƙasar takunkumin hana shigo da makamai. Tun daga lokacin ake ci gaba da sabunta takunkumin tare da ɗora takamaiman hukunci kan wasu mutane da ake dangantawa da ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai da ayyukansu.

  8. Za mu tabbatar Iran da Amurka sun sake komawa teburin sulhu - Pakistan

    Iran

    Asalin hoton, Roberto Schmidt/Getty Images, Iran President Press Office / Handout /Anadolu via Getty Images

    Pakistan ta ce har yanzu tana ƙoƙarin dawo da Iran da Amurka kan teburin tattaunawa domin jaddada yarjejeniyar Islamabad.

    "Burinmu shi ne mu tabbatar da cewa dukkan ɓangarorin sun koma kan yarjejeniyar ta Islamabad," in ji mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Pakistan, Tahir Andrabi, yayin da yake ganawa da manema labarai a yau.

    A cewarsa, Pakistan ta fata ƙasashen biyu su "cika alƙawurransu gaba ɗaya na amfani da ke ƙunshe a yarjejeniyar."

    Amurka da Iran dai sun sanar da cewa sun yi watsi da wannan yarjejeniya, inda suka koma yi wa juna luguden wuta.

    Pakistan dai ce ta shige gaba domin ƙulla yarjejeniyar ta Islamabad, wadda aka sanya wa hannu domin kawo ƙarshen yaƙin.

  9. Mun lalata jiragen yaƙin Amurka ƙirar F-35 guda uku a Jordan - Iran

    Amurka

    Asalin hoton, EPA

    Dakarun juyin-juya-halin Iran wato IRGC sun ce sun lalata gaba ɗaya jiragen yaƙin Amurka kirar F-35 guda uku, sannan ta yi wa wasu guda uku mummunar ɓarna a wani harin makamai masu linzami da ta kai kan sansanin sojin sama na Al-Azraq da ke Jordan.

    Sai dai har zuwa yanzu, Amurka ko Jordan, ko kuma wasu majiyoyi masu zaman kansu, ba su tabbatar da wannan ikirari ba.

    Sashen hulɗa da jama'a na IRGC ya bayyana cewa harin martani ne ga hare-haren sama da Amurka ta kai kan gidaje biyu a tsibirin Qeshm, inda ta ce mutane uku na gida, ciki har da wani yaro, suka mutu, yayin da wasu yara biyu suka jikkata.

    IRGC ta kuma yi ikirarin cewa wasu jami'an sojin Amurka da ma'aikatan fasaha sun mutu a harin da aka kai kan rumfar da ake ajiye da gyaran jiragen yaƙi a sansanin Al-Azraq, amma ba ta bayyana adadin waɗanda suka mutu ba.

    A baya, sojojin Jordan sun sanar da cewa tsarin kariyar sararin samaniyarsu ya tare tare da lalata makamai masu linzami guda biyar da aka harba daga Iran, kuma sun ce harin bai yi sanadin asarar rayuka ba.

    Har zuwa yanzu, Amurka ba ta fitar da wani rahoto da ke tabbatar da lalata jiragen yaƙin F-35 ko kuma asarar rayukan sojojinta a wannan harin ba.

  10. 'Yadda na yi auren Mutu'a na tsawon shekara biyu'

    Mut'a

    Yayin da ake ci gaba da musayar yawu dangane da halasci ko rashin halascin auren mutu'a wata wanda ta yi auren mutu'a na tsawon shekara biyu ta shaida wa BBC yadda al'amarin ya faru.

    A ƙarshen makon da ya gabata ne dai wani bidiyo na limamin babban masallacin Abuja, Farfesa Ibrahim Maƙari ya nuna yadda malamin ke magana kan wata amsar tabbaya da ya ce ya bai wa ɗalibansa da ke harkokin rayuwa a ƙasar waje.

  11. 'Mun haɗa kuɗin fansa sama da miliyan 150 amma ba a sako ƴan'uwanmu ba'

    Soja

    Asalin hoton, @HQNigerianArmy

    Kimanin wata biyar kenan bayan da ƴan bindiga suka dira a ƙauyen Woro na jihar Kwara, inda suka yi wa mutane ɗaya daga cikin kisan gilla mafi muni da aka gani a baya-bayan nan a Najeriya.

    Ɓarnar da ƴan bindigar suka yi ta ƙazanta, lamarin da ya janyo hankalin ɗaukacin al'ummar Najeriya da ma masu sanya ido kan harkar tsaro a ƙasashen ƙetare.

  12. Iran ta sake kai sabbin hare-hare a Kuwait da Jordan

    IRAN

    Asalin hoton, IRNA

    Iran ta ci gaba da kai hare-hare kan wurare daban-daban a yankin gabas ta tsakiya, bayan sojojin Amurka sun bayyana cewa sun kai jerin hare-haren sama da suka kai kan Iran cikin daren jiya.

    Kuwait ta ce wani makami mai linzami da Iran ta harba ya faɗa kan wani gini a arewacin ƙasar, inda ya kashe mutum ɗaya.

    Sojojin Jordan kuwa sun ce sun harbo makamai masu linzami guda biyar da Iran ta harba.

    Tun da farko, sojojin Amurka sun ce sun kai hari kan wurare da dama mallakin rundunar juyin-juya-halin Iran wato IRGC, a matsayin martani ga harin makamai masu linzami da Iran ta kai ranar Talata kan wani sansanin sojojin Amurka da ke Jordan.

    Kafofin yaɗa labarai na Iran sun ce hare-haren na baya-bayan nan da Amurka ta kai sun kashe mutane uku, ciki har da wani yaro.

  13. 'Hana yara shan sukari na inganta lafiyar ƙwaƙwalwarsu'

    Yara

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani sabon bincike da aka gudanar ya gano shaidar da ke nuna cewa rage yawan shan siga ga yara daga shekara biyu na matuƙar taimakawa wajen kare lafiyar ƙwaƙwalwarsu na tsawon gomman shekaru.

    Binciken wanda jami'ar kimiya da fasaha ta Hong Kong ta gudanar ya yi nazari kan tasirin sukarin a Birtaniya bayan yaƙin duniya na biyu.

    Sakamakon ya nuna mutanen da suke yara a lokacin yaƙin da suka taƙaita shan sukari sun samu kariya daga kamuwa da cutar mantuwa da kusan kashi ashirin da uku cikin ɗari.

  14. Amurka za ta fitar da dala miliyan 600 domin tallafawa allurar riga-kafi

    Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka za ta fitar da kudade har dala miliyan dari shida nan ba da jimawa ba domin Ƙungiyar Gavi, wacce ke taimaka wa kasashe masu tasowa wajen samar da allurar riga-kafi.

    Tunda farko Sakataren lafiyar Amurka Robert Kennedy ne ya riƙe kuɗaden bayan ya yi amannar cewa Gavi na amfani da sinadaran da aka daina amfani da su wadanda ke da haɗari ga lafiyar dan'adam.

    Sai dai Gavi ta ce matakin nasa ya jefa miliyoyin yara cikin hadarin kamuwa da cututtukan da ake iya ɗauka.

  15. Rasha ta kai mana hare-hare - Ukraine

    Ukraine

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Ukraine ta ce Rasha ta kai mata hare-hare a yankuna uku na ƙasar.

    Hakan na zuwa ne bayan gargadin da shugaba Zelensky ya yi na cewa Rashar na shirin kai masu gagarumin hari.

    Wakiliyar BBC ta ce magajin garin birnin Kyiv ya ce Rasha ta kai hare-haren makamai masu linzami, inda ya ce an samu rahoton gobara a gudunma biyu na birnin.

    Ya zuwa yanzu mutum biyar ne ciki har da yara biyu suka rasu sakamakon hare-haren, sai kuma gidaje da suka rushe.

  16. Amurka ta ce ta kai hare-hare masu ƙarfi a Iran

    Amurka

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Amurka ta ce ta fara kai sabbin jerin hare-hare masu ƙarfi da tasiri kan Iran.

    Hakan na zuwa ne bayan da shugaba Trump ya sha alwashi tare da yin alƙawarin yi wa Iran din luguden wuta mafi muni.

    Kafofin watsa labaran Iran sun ruwaito cewa an kai hari kan matatun man fetur biyu na ƙasar.

    Wakilin BBC ya ce an samu rahotannin fashewar abubuwa a sassa daban-daban na Iran Iran ma ta bada tabbacin kai hare-hare kan kadadarorin Amurka dake Jordan da kuma kan jiragen ruwa a mashigar Hurmuz.

  17. Farawa

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa, barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.