Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 6/08/2026

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 6 ga watan Agustan 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Muslim Muhammad Yusuf

  1. Rasha ta ce ta lalata jirage marasa matuƙa 605 da Ukraine ta harba cikin dare

    Ma'aikatar Tsaron Rasha ta ce dakarunta sun kakkabo jiragen marasa matuƙa 605 na Ukraine a hare-haren da ta kai cikin daren Laraba.

    A cewar ma'aikatar, an daƙile hare-haren ne a yankuna da dama, ciki har da Moscow da Yaroslavl, inda ɗaya daga cikin manyan matatun man Rasha, Slavneft-Yanos, take.

    Rahotanni sun ce an ga baƙin hayaƙi mai yawa na tashi sama a birnin Yaroslavl bayan harin da jiragen marasa matuƙa da Ukraine suka kai.

    Gwamnan yankin, Mikhail Evraev, ya ce wannan shi ne hari mafi girma da yankin ya taɓa fuskanta, kumaan lalata jirage marasa matuƙa 92 a yankin kaɗai.

    A gefe guda kuma, jami'an Ukraine sun ce hare-haren Rasha sun kashe mutum uku a birnin Balakliya, yayin da wasu 12 suka jikkata a yankin Sumy.

  2. Iraniyawa mutane ne masu taurin kai - Mataimakin Shugaban Amurka

    Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, ya ce yana ganin Iraniyawa a matsayin wasu mutane masu taurin kai, inda ya ce hakan na daga cikin ƙalubalen da ake fuskanta wajen warware rikicin da ke tsakanin ƙasarsa da Iran.

    A wata hira da ya yi da tashar Fox News, Vance ya mayar da martani kan sukar da wasu Amurkawa ke yi game da yadda gwamnatin ƙasar ke tafiyar da yaƙin da Iran.

    Ya ce akwai rarrabuwar kawuna a cikin gwamnatin Iran, kuma wani ɓangare na shugabannin ƙasar na son a ci gaba da tattaunawa, yayin da wani ɓangaren masu tsattsauran ra'ayi ke son a ci gaba da yaƙi.

    Vance, wanda ya jagoranci tawagar Amurka a tattaunawar Islamabad, yana da yaƙinin cewa daga ƙarshe "komai zai ƙare ne ta hanyar da za ta amfani al'ummar Amurka."

    Sai dai ya bayyana cewa ana samun ci gaba da koma baya a rikicin da ake yi da Iran

    Wasu rahotanni sun ce shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, na iya kai ziyara Pakistan cikin 'yan kwanaki masu zuwa.

    Sai dai gwamnatin Iran ba ta tabbatar ko musanta waɗannan rahotanni ba.

  3. Ukraine ta ce ta kai hari kan matatun mai biyu a Rasha

    Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya ce dakarun ƙasarsa sun kai hare-hare kan matatun mai biyu da ke cikin Rasha.

    A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Zelensky ya ce sojojin Ukraine sun kai hari kan matatar mai ta Slavneft-Yanos da ke birnin Yaroslavl, da kuma matatar Bashneft-Novoil da ke yankin Bashkortostan.

    Tun da farko, rahotanni sun ce an ga baƙin hayaƙi na tashi daga yankin matatar mai ta Yaroslavl bayan hare-haren jiragen saman marasa matuƙa na Ukraine.

    Zelensky ya kuma ce dakarunsa sun kai hari kan kwale-kwalen sintiri guda biyu na sojojin Rasha da kuma wasu jiragen ruwan Rasha a Baharul Aswad.

    Har yanzu hukumomin Rasha ba su yi martani kan ikirarin Ukraine ba.

  4. Infantino ya nemi afuwa kan shirin sayar da hannun jarin Kofin Duniya

    Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), Gianni Infantino, ya nemi afuwa kan kura-kuran da ya tafka dangane da wani shiri mai cike da ce-ce-ku-ce na sayar da hannun jari a wasu gasannin ƙwallon ƙafa ga masu zuba jari masu zaman kansu.

    Sai dai duk da sukar da ya fuskanta, Infantino zai ci gaba da riƙe muƙaminsa bayan ya samu goyon bayan manyan shugabannin FIFA a wani taron da aka gudanar a Maroko.

    Da alama ya shirya sake neman kujerar a karo na hudu da za a gudanar da zaɓe a watan Maris na shekarar 2027.

    Infantino ya gayyaci mambobin kwamitin gudanarwar FIFA zuwa hedikwatar hukumar ta nahiyar Afirka da ke Maroko a ranar Laraba, domin tattauna batun bayan ƙorafe-ƙorafen da aka yi kan yunƙurin sayar da hannun jari a gasannin ƙwallon ƙafa.

  5. Amurka da Oman ba su ce komai ba kan buɗe sabuwar hanyar zirga-zirga a Mashigar Hurmuz

    Har yanzu Amurka da Oman ba su ce komai ba kan iƙirarin Iran na cewa tana dab da cimma yarjejeniya da Oman kan wata sabuwar hanyar zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Hurmuz.

    Mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran ya bayyana haka a ranar Laraba, inda ya ce Iran da Oman sun riga sun amince da taswirar sabuwar hanyar da za a riƙa amfani da ita a mashigar.

    Sai dai ya ƙara da cewa aiwatar da yarjejeniyar zai dogara ne kan rashin tsoma bakin wasu ƙasashe.

    Sai dai wakilin BBC ya ce ko da an cimma irin wannan yarjejeniya, tana buƙatar samun goyon bayan Amurka kafin ta iya yin tasiri a aikace.

  6. Gari Ya Waye!!!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis. Gari ya waye a Najeriya da Nijar da wasu sassan duniya.

    A wannan shafin namu na BBC Hausa, za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Muslim Muhammad Yusuf tare da sauran abokan aiki za mu kasance da ku.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.