Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 3/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin, 3 ga watan Agustan 2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Iran ta ce ba ta wata tattaunawa da Amurka a halin yanzu

    Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce a halin yanzu babu wata tattaunawa da ke gudana tsakanin Iran da Amurka, duk da cewa Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa za a fara sabbin tattaunawa a yau Litinin.

    Baghaei ya bayyana cewa a yanzu Tehran ta fi mayar da hankali kan tattaunawar da take yi da Oman game da mashigar Hormuz, wadda ta shafe kwanaki takwas tana gudana.

    Ya ce duk wata fahimta da ake samu da Oman ba tana nufin an buɗe mashigin Hormuz ba har sai an tabbatar da tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin.

    Baghaei ya kuma jaddada cewa rufe mashigin Hormuz ya biyo bayan hare-haren Amurka da Isra'ila ne, ba saboda saɓani tsakanin Iran da Oman ba.

    A cewarsa, Iran da Oman na tattaunawa kan wata sabuwar hanyar zirga-zirgar jiragen ruwa.

  2. Iran ta kashe mutum biyu kan zargin yi wa Isra'ila leƙen asiri

    Hukumar shari’ar Iran ta sanar da aiwatar da hukuncin kisa kan Omid Behzad da Pouria Safvat a safiyar Litinin, bayan kotu ta same su da laifin yi wa Isra’ila leƙen asiri.

    A cewar kamfanin yaɗa labaran ma’aikatar shari’ar Iran, Mizan, mutanen biyu sun kasance suna tattarawa tare da aika wa hukumar leƙen asirin Isra’ila ta Mossad bayanai, hotuna da kuma bayanan wuraren da cibiyoyin soji da na tsaro na Iran suke.

    Mahukuntan Iran sun ce irin waɗannan bayanai sun taimaka wajen gudanar da ayyukan leƙen asiri da suka shafi tsaron ƙasar.

    Sai dai ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama da wasu lauyoyi sun dade suna nuna damuwa kan yadda ake gudanar da irin waɗannan shari’o’i a Iran, suna zargin cewa ana gaggauta aiwatar da hukuncin kisa ba tare da tabbatar da cikakken tsarin shari’a mai adalci ba.

    Sun kuma ce rashin bai wa waɗanda ake tuhuma damar samun lauya yadda ya kamata na daga cikin matsalolin da ke haifar da tambayoyi kan adalcin irin waɗannan hukunci.

  3. Iran na ƙarfafa hulɗa da Saudiyya da Pakistan kafin tattaunawarta da Amurka

    Iran na ci gaba da ƙarfafa hulɗarta da Saudiyya da Pakistan ta hanyar tattaunawa da manyan jami'an ƙasashen biyu, a daidai lokacin da ake sa ran fara sabon zagayen tattaunawa tsakanin Tehran da Washington cikin sa'o'i masu zuwa.

    Kamfanin dillancin labaran gwamnatin Iran (IRNA) ya ruwaito cewa ministan harkokin wajen ƙasar, Abbas Araqchi, ya yi tattaunawa ta biyu a ranar Lahadi da takwaransa na Saudiyya, Faisal bin Farhan Al Saud.

    Haka kuma ya yi wata tattaunawa ta wayar tarho da ministan harkokin wajen Pakistan, sannan daga bisani ya tuntubi shugaban rundunar sojin Pakistan, Field Marshal Asim Munir, wanda ake kallon sa a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu tasiri a harkokin tsaro da siyasar ƙasar.

    Wadannan tattaunawa na zuwa ne bayan shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa za a fara sabon zagayen tattaunawa tsakanin Amurka da Iran, inda za a mayar da hankali kan batutuwan mashigin ruwa na Hormuz da kuma shirin nukiliyar Iran.

  4. Trump ya sanar da fara sabbin tattaunawa da Iran a yau Litinin

    Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa za a fara sabbin tattaunawa tsakanin Amurka da Iran a yau Litinin, bayan sanarwar da ya yi a daren jiya game da janye wasu hare-haren da aka shirya kai wa Iran.

    Trump ya ce a halin yanzu akwai fahimta kan batun mashigar Hormuz, kuma yana da yakinin cewa za a cimma yarjejeniya kan shirin nukiliyar Iran.

    Trump ta fadi hakan ne yayin da yake magana da manema labarai a cikin jirgin shugaban ƙasa na Air Force One a ranar Lahadi.

    A gefe guda kuma, ministocin harkokin wajen Iran, Saudiyya, Pakistan, Qatar da Jordan na ci gaba da gudanar da tattaunawa da shawarwari, waɗanda ake ganin sun fi mayar da hankali kan tattaunawar da ke tsakanin Tehran da Washington.

  5. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.