KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Alhamis 16/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Alhamis 16/07/2026

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. 'An kashe wani babban injiniya Zaporizhzhia'

    Kamfanin makamashin nukiliya na gwamnatin Rasha ya ce an kashe babban injiniyan tashar samar da wutar lantarki ta nukiliya a yankin Zaporizhzhia, da ke Ukraine, wadda Rasha ke iko da ita, a harin da wani jirgin mara matuƙi na ƙasar Ukraine ya kai kusa da tashar.

    Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) ta ce an sanar da ita game da mutuwar jami'in, tare da sake nanata kiranta da a dakatar da duk wani hari da ake kai wa kusa da cibiyoyin nukiliya da ma'aikatansu.

    Sojojin Rasha sun ƙwace iko da tashar Zapo-rijiya ne a makonnin farko na mamayar da Moscow ta ƙaddamar kan Ukraine a shekarar 2022.

    A wani labarin kuma, Rasha ta sake kai wa Kyiv babban birnin Ukraine, hare-haren makamai masu linzami , inda aka ba da rahoton fashe-fashe da dama a safiyar yau Alhamis.

  2. An ji ƙarar sabbin fashewa a Iran

    sojoji

    Asalin hoton, ..

    An ji ƙarar fashewar abubuwa a sassa daban-daban na Iran, ciki har da yankunan da ke nesa da Tekun Fasha, yayin da rundunar sojin Amurka ta sanar cewa ta ƙaddamar da wani sabon zagayen hare-hare.

    A babban birnin ƙasar, Tehran, an yi amfani da na'urar kakkaɓo makamai masu linzami yayin da a birnin Ah-vaz da ke kusa da arewacin Tekun Fasha.

    Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun ce an kwashe marasa lafiya daga wani asibiti saboda hare-haren makamai masu linzami da aka kai a kusa da yankin.

    Babban mai shiga tsakani na Iran a tattaunawarta da Amurka, Mohammed Bagher Qalibaf, ya fitar da wata sanarwa yana mai cewa ƙasarsa na ci gaba da bin tafarkin tattaunawa da kuma yaƙi a lokaci guda, amma ya zama dole Iran ta ci gaba da riƙe ikon kula da mashigin ruwan Hormuz.

    Iran ta mayar da martani tana mai cewa ta mayar da hankali ne wajen lalata cibiyoyin sojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokacin domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muek wallafawa