Iran ta yi iƙirarin lalata wasu cibiyoyin Amurka a yankin Gulf

Asalin hoton, Reuters
Dakarun juyin juya halin Iran sun bayyana cewa sun lalata na;urorin sadarwar Amurka biyu a ƙasar Oman.
Cikin wata sanarwar da rundunra ta wallafa a shafukanta na sada zumunta, ta ce rundunar sojin ruwanta ta lalata na'urar da ke kula da sadarwar jirage a tashar ruwa ta Salalah da kuma wadda ke tashar Ghanem duka a Oman da safiyar yau Juma'a.
Sanarwar ta jaddada cewa Iran za ta ci gaba da ɗaukar matakan martani, kuma mashigar Hormuz za ta ci gaba da kasancewa ƙarƙashin ikon dakarun sojin ruwa na rundunar juyin juya halin.
IRGC ta kuma ce ta kai hari kan sansanin sojin Amurka na Al-Tanf da ke kudancin Siriya.
Rundunar ta ce ta kai harin ne a matsayin martani ga kisan sojojinta a harin Iranshahr.
''Dakarun sojin sama na rundunar IRGC sun kai hari kan sansanin sojojin Amurka na musamman a Al-Tanf, da na'urorin sadarwar jirage da kan jirage na musamman masu saukar ungulu da wasu sojojin na Amurka'', in ji sanarwar ta IRGC.
To sai dai kakakin rundunar sojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya, CENTCOM ya shaida wa kafar yaɗa labarai na Al Jazeera cewa hare-haren an Iran kan ƙasashen yankin Gulf ''ba su haifar da wani lahani da ayyukan sojojin ba''.



