Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 02/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 02 ga watan Agustan 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. A shirye muke mu mayar da martani mai tsauri ga duk wani hari - Iran

    Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, ya bayyana cewa ƙasarsa a shirye take ta mayar da martani mai ƙarfi ga duk wani hari da za a kai mata, yayin da ya yi gargaɗi ga Amurka kan duk wata “kasada” da za ta iya ƙara tayar da rikici a yankin.

    Araghchi ya bayyana hakan ne a tattaunawar waya da ya yi da ministan harkokin wajen Turkiyya da kuma babban kwamandan sojojin Pakistan, inda ya jaddada cewa Iran za ta kare kanta idan aka kai mata hari.

    Haka kuma ya shaida wa ministan harkokin wajen Saudiyya cewa duk wani hari da Amurka ko Isra’ila za su kai, ko kuma wanda wasu ƙasashen yankin za su goyi baya, zai fuskanci martani mai tsauri daga Iran.

    Wannan na zuwa ne yayin da rahotanni ke nuna yiwuwar Amurka ta ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Iran, yayin da ofisoshin jakadancin Amurka a Bagadaza da Erbil suka gargadi ‘yan ƙasarsu da su kasance cikin shirin ficewa daga yankin Gabas ta Tsakiya idan buƙatar hakan ta taso.

  2. Sojojin Najeriya sun kama wasu da ake zargi da kai wa dakarunsu hari a Delta

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta ƙarƙashin rundunar Operation UDOKA sun sanar da kama wasu manyan mambobin wata ƙungiyar masu aikata laifuka da ake zargi da kai wa sojoji kwanton ɓauna a ranar 4 ga Mayun 2026 a jihar Delta.

    Harin ya yi sanadin mutuwar soja ɗaya tare da jikkata wani.

    A wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce bayan harin ne sojoji suka ƙaddamar da jerin samame bisa bayanan sirri domin kamo waɗanda suka aikata laifin da kuma ƙwato makaman da aka sace.

    Hakan ya kai ga cafke waɗanda ake kira Chiboy, Marathon da Onowu bayan sun tsere zuwa garin Oleh da ke jihar Delta.

    Sojojin sun ce waɗanda aka kama sun jagorance su zuwa maɓoyarsu da ke Aggah Plantation a jihar Rivers da kuma Umudike Plantation, inda aka ɓoye makaman da aka sace da sauran makaman da ake amfani da su wajen aikata laifuka.

    A yayin samamen, an ƙwato bindigogi da alburusai da dama da sauran kayan aikinsu.

    Rundunar ta ce ana ci gaba da bincike kan waɗanda ake zargin kafin gurfanar da su a gaban kotu, tare da jaddada aniyarta na ci gaba da yaƙi da masu aikata laifuka domin tabbatar da zaman lafiya a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya.

  3. Saudiyya ta buƙaci Trump kada ya ƙaddamar da harin da ake shiri kan Iran

    Yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya buƙaci Donald Trump da kada ya ƙaddamar da babban harin da ake shiri kai wa Iran, saboda fargabar ƙarin taɓarɓarewar tsaro a yankin, kamar yadda rahoton Axios ya bayyana.

    A cewar rahoton, Bin Salman ya nemi Trump ya rage ƙamari tare da kauce wa kai hare-haren, yayin da Saudiyya kuma ta nemi ƙarin bayani kan shirin ayyukan sojin Amurka.

    Rahoton ya ce Trump na duba yiwuwar kai hari kan cibiyoyin makamashin Iran a kwanaki masu zuwa, amma har yanzu bai yanke hukunci na ƙarshe ba.

    A lokaci guda, Qatar, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Turkiyya da Pakistan na ƙoƙarin rage rikicin da ke tsakanin Amurka da Iran.

    An kuma samu wasu ci gaba a tattaunawar da ake yi domin sake buɗe mashigar Hormuz, ko da yake har yanzu ba a tabbatar ko hakan zai hana rikicin ƙara ta'azzara ba.

  4. Ba za mu bari a yi amfani da ƙasarmu wajen kai hari kan maƙwabta ba - Iraq

    Firaministan Iraq, Mohammed Shia al-Sudani, ya ce gwamnatinsa ba za ta amince a yi amfani da ƙasar ba domin kai hare-hare ko barazana ga ƙasashen maƙwabta.

    A yayin wani taron gaggawa da ya jagoranta domin duba halin tsaro a yankin, Sudani ya ba da umarnin kafa kwamitin tsaro na haɗin gwiwa da kuma samar da matakan hana sake faruwar irin waɗannan ayyuka.

    Ya kuma umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da bin doka, ƙarfafa zaman lafiya da tsaro, tare da kare ikon mallakar ƙasar da kyakkyawar alaƙa da maƙwabta.

    Sanarwar taron ta ce dakarun Iraq suna cikin shirin ko-ta-kwana don dakile duk wani yunƙuri da za a yi daga cikin ƙasar domin cutar da ƙasashen da Baghdad ta bayyana a matsayin “ƙawayenta da ‘yan’uwanta.

  5. Iran ta ce a shirye take tsaf ta kare muradu da tsaron ƙasarta

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta ce ƙasar a shirye take ta kare muradunta da tsaron ƙasarta bayan sabbin barazanar da Amurka ta yi na kai mata hari.

    A cikin wata sanarwa, Iran ta bayyana hare-haren Amurka a matsayin “haramtattu”, tare da zargin cewa an kai su ne da haɗin gwiwar Isra’ila da wasu ƙasashen yankin.

    Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka da wasu ƙawayenta na yankin suna amfani da batun zirga-zirgar jiragen ruwa a kudancin yankin a matsayin kariya ga ayyukan soja.

    Iran ta jaddada cewa ba ta da wata gaba da ƙasashen yankin Tekun Fasha, tana kuma neman kyakkyawar dangantaka da su.

    Ta kuma ce duk wani martani da take bayarwa zai kasance kan waɗanda suka kai mata hari ne, ba kan ƙasashen yankin ba.

    Sanarwar ta zo ne yayin da ofisoshin jakadancin Amurka a Gabas ta Tsakiya suka gargadi ‘yan ƙasarsu da su kasance cikin shiri saboda yiwuwar ƙarin tashin hankali a yankin.

  6. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da Safiyar ranar Lahadi.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.