Kotun ƙolin Najeriya ta sanya ranar Alhamis 30 ga watan Afirilu, domin yanke hukunci kan shari'ar shugabancin da ta mamaye jam'iyyar adawa ta ADC.
Kotun ƙolin ta ɗage sauraron ƙarar tun da fari abin da ya sa jam'iyyar adawar ta shigar da ƙarar alƙalin alƙalin kasar kan shari'ar tana cewa tana bahu lokacin da za a yi ta ɗaga sauraron shari'ar ta ta.
A yau Laraba ne kuma, kotun ta sanar da cewa za ta yanke hukuncin ne a gobe Alhamis da misalin ƙarfe biyun rana.
David Mark, wanda yake shugabantar ɓangare guda na ADC, ya ƙalubalanci hukuncin 12 ga watan Maris na kotun ɗaukaka ƙara, wadda ta umarci a koma yadda tsarin jam'iyyar yake gabanin kai ƙarar.
A ƙarar da ya ɗaukaka, tsohon shugaban majalisar dattijan ya ce kotun ta wuce iyakarta kan hukuncin, ya kuma dage kan cewa wannan rikicin na cikin gida ne, wanda doka ba ta baiwa kotun hurumin shiga ba.
Wasu mambar jam'iyyar ne suka shigar da ƙarar, wanda wani matashi Nafi'u Gombe da ya yi ikirarin shugabancin jam'iyyar yake jagoranta.
Cikin waɗanda aka shigar ƙasarar akwai Sakatern jam'iyyar na ƙasa Rauf Aregbesola, da Hukumar Zaɓe ta ƙasa INEC da tsohon shugaban jam'iyyar Ralp Nwosu.
Mark a cikin buƙatarsa na son kotu ta daina amincewa da duk wani tsagen jam'iyyar indai ba wanda yake jagoranta ba, har sai hukuncin ƙarshe da aka yanke na gobe Alhamis.
Sai dai Nafi'u da abokan da suke tare sun roki kotun ta yi watsi da ɗaukaka ƙarar da Mark ya yi, suna cewa hukuntun kotun baya shi ne daidai.
Hankalin 'yan Najeriya dai na kan wannan shari'a, musamman a wannan lokacin da ake yi wa ADC kallon babbar jam'iyyar adawa a kasar, wadda ta haɗa manyan jiga-jigan 'yan siyasar da suka yi takara da shugaba Bola Tinubu a 2023.