Gwamnatin Amurka ta sanya sunan wani ɗan Najeriya mazaunin Legas, Muhammad Mukhtar Adamu, cikin jerin mutanen da take zargi da taimaka wa ƙungiyar ISIS a Afrika ta Yamma.
Ta ce yana amfani da kamfanoninsa na canjin kuɗi wajen tura kuɗaɗe ga ƙungiyar.
A wata sanarwa da Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fitar ranar Litinin, mai magana da yawunta, Thomas Pigott, ya ce zargin ya shafi mutum uku da kamfanoni shida da ake zargi da taimaka wa ƙungiyar ISIS wajen gudanar da harkokin kuɗaɗenta a sassa daban-daban na duniya.
Daga cikin kamfanonin shida, uku na Najeriya ne, inda biyu ke jihar Legas yayin da ɗaya ke jihar Kano.
Kamfanonin sun haɗa da Nine To Nine Exchange Bureau De Change Limited da ke harabar filin jirgin sama na Legas, da Manhattan Bureau De Change Limited da ke titin Murtala Mohammed a Kano, da kuma Generation Currency Bureau De Change Limited da ke Legas.
Amurka ta kuma sanya takunkumi kan kamfanonin canjin kuɗin guda uku da ta ce Adamu ne ke mallaka ko kuma yake sarrafa su.
Hukumar Kula da Kadarorin Ƙetare ta Amurka (OFAC) ta Sanarwar ta ce mutanen da kamfanonin da aka aka gano sun fito ne daga ƙasasheirinsu Faransa, Syria, Turkiya da Najeriya.
Bayanin ya ce Adamu na zaune ne a gida mai lamba 45, da ke titin Abimbola, kusa da Capital Road, ta yankin Agege a jihar Legas.
Ta kuma ce an haife shi a Najeriya a ranar 2 ga Agustan 1990, amma kuma wasu bayanai sun nuna ranar 3 ga Agustan shekarar.
Sauran mutanen biyu da aka sanya wa takunkumin su ne Abderrahmane Miloud, wanda aka fi sani da Ghazi Ibrahim, ɗan ƙasar Faransa da ake zargi da gudanar da mu'amaloli da mutanen da ke da alaƙa da ISIS tare da bayar da bayanai kan abubuwan fashewa ga magoya bayan ƙungiyar.
Na uku kuwa shi ne Abdelhakim Boukich, wanda aka fi sani da Babili Muhammad, wanda Amurka ta bayyana a matsayin mai taimaka wa masu tsattsauran ra'ayi da kuɗi daga ƙasar Siriya, kuma tana zarginsa da sarrafa wata manhajar musayar kuɗin Bitcoin da ake amfani da ita wajen mu'amalolin da ke da alaƙa da ISIS.