Trump ya ce yana sa ran Isra'ila ta dakatar da duk wasu hare-hare a Lebanon
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce yana sa ran a tsagaita wuta gaba ɗaya a dukkan angarorin da ke rikici a Gabas ta Tsakiya, ciki har da tsakanin Isra'ila da ƙungiyar Hezbollah a Lebanon.
A wani sabon saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce yana fatan ƙasashen yankin za su cika alƙawuran da suka ɗauka domin tabbatar da tattaunawar zaman lafiya ta gudana yadda aka tsara.
"Muna sa ran a tabbatar da tsagaita wuta baki ɗaya a dukkan ɓangarori, ciki har da a Lebanon tsakanin Hezbollah da Isra'ila," in ji shi
Sashe na farko na yarjejeniyar da Iran da Amurka suka rattaba wa hannu ya jaddada buƙatar dakatar da duk wasu hare-hare a dukkan wuraren da rikicin ya shafa, ciki har da Lebanon.
Sai dai duk da hakan, Isra'ila ta bayyana cewa ba ta da shirin janye dakarunta daga Lebanon.
Haka kuma kafafen yaɗa labarai na gwamnatin Lebanon sun ruwaito cewa Isra'ila ta kai hare-hare a wasu yankunan kudancin ƙasar a yau.