'Adadin ɗabilan da aka sace daga Borno sun kai 50'
Bayanan da ke fitowa daga Najeriya na cewa fiye da ɗalibai 50 ne aka bayar da rahoton garkuwa da su a wasu hare-hare da aka kai wa makarantu a yankin arewa maso gabashin ƙasar aranar Juma'a
Rahotonni na cewa mafi yawan yaran ƴan tsakanin shekara biyu zuwa biyar ne, waɗanda aka sace daga makarantun nazare.
Iyaye a ƙauyen Mussa na jihar Borno, na cikin zaƙuwar jiran bayanai game da yaran nasu.
Kawo yanzu dai babau wanda ya ɗauki alhakin satar ɗaliban, yayin da rahotonni suka ce tuni wasu iyayen suka fara tsarewa daga ƙauyukan .
Shaidu sun ce maharan na amfani da yaran a matsayin garkuwa domin guje wa hare-haren jami'an tsaro, bayan da suka tsere da su a kan babura.