Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Jana’izar Khamenei da sauran abubuwan da ke faruwa a duniya 05/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwa kan Jana’izar Khamenei da sauran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 5 ga watan Yulin 2026

Rahoto kai-tsaye

Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Za mu ci gaba da girmama ƴancin gudanar da addini a Najeriya - Tinubu

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada cewa gwamnatinsa na ba da fifiko wajen tabbatar fahimtar juna a tsakanin addinai da kuma inganta zaman lafiyar ƙasar.

    Shugaban ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a Abuja yayin da ya karɓi baƙuncin Archbishop Paul R. Gallagher, sakataren hulɗa da ƙasashe da ƙungiyoyi na Vatican, wanda ya ziyarci shugaban tare da rakiyar ministan harkokin wajen Najeriya, Ambasada Bianca Ojukwu.

    Shugaba Tinubu ya ce tattaunawa domin fahimta juna a tsakanin addinai ita ce hanya mafi dacewa wajen magance ƙalubalen tsaron da ƙasar ke fuskanta.

    Ya shaida wa Archbishop ɗin cewa yana da dadaddiyar kyakkyawar alaƙa da Cocin Katolika tun lokacin da yake gwamnan Jihar Legas. Ya ce yana matuƙar alfahari da gudummawar da Cocin ke bayarwa a fannonin ilimi da kiwon lafiya.

    Tinubu ya kuma shaida wa baƙon cewa rundunar sojin Najeriya ta samu gagarumin ci gaba a baya-bayan nan, sannan ya ƙara da cewa za su ci gaba da ƙoƙari domin tabbatar da nasarar.

    A nasa jawabin, Archbishop Gallagher ya ce ya ziyarci Najeriya ne domin bikin cika shekara 50 da ƙulla hulɗar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Cocin Katolika, sannan ya ce Najeriya ƙasa ce mai matuƙar muhimmanci ga Cocin saboda yawan mabiya da kuma ƙarfinta.

    Ya kuma isar da godiyar Paparoma Leo XIV ga Shugaba Tinubu bisa halartar bikin rantsar da shi. Haka kuma ya bayyana jin daɗinsa da irin ci gaban da Jami'ar Veritas, wadda Cocin Katolika ta kafa a Abuja, ta samu.

  2. Waɗanda suka rasu a girgizar ƙasar Venezuela sun haura 3,000

    Gwamnatin Venezuela ta ce adadin mutanen da aka tabbatar sun mutu sakamakon munanan girgizar ƙasar biyu da suka afku a ƙarshen watan da ya gabata a kasar sun kai kusan mutum dubu uku.

    Sai dai wata ƙididdigar da ba ta hukuma ba ta nuna cewa har yanzu sama da mutum dubu 40 ba a san inda suke ba.

    Wakiliyar BBC ta ce, masu aikin ceton gaggawa a arewacin Venezuela na ci gaba da aikin zakulo gawarwaki daga ƙarƙashin baraguzan gine-ginen da suka rushe, a yayin da ake ganin kusan babu sauran fatan gano waɗanda suka tsira.

    Shugaban Majalisar Dokokin Venezuela, Jorge Rodriguez, wanda kuma ɗan'uwan shugabar riƙon ƙwarya ƙasar ne, ya jaddada cewa ana ci gaba da ayyukan ceto a yankunan da bala'in ya shafa.

  3. Ranar Litinin za a zaga da gawar Khamenei domin ban-kwana da ƴan ƙasar

    An ayyana yau Lahadi a matsayin ranar hutu ga daukacin al'ummar Iran ,a yayin da ake ci gaba da shirye shiryen jana'izar jagoran addinin ƙasar da ya rasu, Ayatullah Ali Khamenei.

    Ana sa ran gudanar da addu'oi a kan gawarsa da misalin ƙarfe shida na safe agogon GMT.

    Wakiliyar BBC ta ce a ranar Litinin ana tsammanin za a gudanar da babban taro inda za a zaga da akwatin gawarsa akan titunan birnin Tehran, kuma ana sa rana miliyoyin mutane za su fito domin bankwanda da gawar.

    Ana sa ran binne Ayatullah Ali Khamenei a garinsa na haihuwa, wato Mashhad, a ranar Alhamis.

    Rahotannin kafafen yaɗa labaran Iran sun ce Ayatollah Jafar Sobhani Tabrizi ne zai jagoranci addu'ar Khamenei da za a gudanar a harabar Mosalla da ke Tehran.

  4. Farawa

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da wannan safiya ta ranar Asabar.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.