Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Mourinho ya sake karɓar aikin kocin Real Madrid kaka uku

Wannan shafi ne da zai ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa daga Litinin 25 zuwa Lahadi 31 ga watan Mayun 2026.

Taƙaitattu

  • Messi zai buga wa Argentina gasar kofin duniya karo na shida jimilla
  • Konate zai bar Liverpool da zarar yarjejeniyarsa ta kare a ƙungiyar
  • Arsenal na shirin tsawaita kwantiragin koci Mikel Arteta
  • Barca za ta dauki Hincapie, Man U da Chelsea na neman Scott
  • Valpato ya zaɓi buga wa Australia tamaula maimakon Italiya
  • Wani bincike ya amince a ci gaba da aiki da VAR amma a Inganta ta
  • Ku shiga zaurenmu na BBC Hausa WhatsApp
  • Ana ci gaba da yin gumurzu a gasar tennis ta French Open
  • Za ku iya tafka muhara a shafnmu na sada zumunta a BBC Hausa Facebook

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Mourinho ya sake karɓar aikin kociyan Real Madrid kan yarjejeniyar kaka uku, Real Madrid

    Jose Mourinho ya sanya hannu kan kwantiragin shekara uku, domin sake zama sabon kocin Real Madrid.

    Sai dai ba za a gabatar da shi a hukumance ba sai bayan zaben shugaban ƙungiyar da za a gudanar ranar 7 ga watan Yuni.

    Duk da haka, kwantiragin Mourinho zai fara aiki ne kawai idan shugaba, Florentino Perez ya ci gaba da rike mukaminsa.

    Perez ya sanar da za a gudanar da sabon zaben ne a wani taron manema labarai na musamman da aka yi a farkon wannan watan, inda ya soki ƴan jarida da kuma La Liga, yana mai cewa akwai “tsarin yaki” da ake yi a kansa.

    Perez mai shekaru 79 yana shugabantar Real Madrid tun 2009, bayan nan kuma ya taba rike mukamin tsakanin 2000 zuwa 2006. Sai dai ƙungiyar ta kammala kakar wasa biyu a jere ba tare da lashe kofi ba.

    Attajiri, Enrique Riquelme ne ke kalubalantar Perez a zaben shugaban Real Madrid na farko cikin shekaru 20 da aka samu hamayya, ko da yake ana sa ran Perez zai sake yin nasara.

    Mourinho ya bar aikinsa na kocin Benfica, inda ya karbi ragamar ƙungiyar a watan Satumba kuma ya kai ta matsayi na uku a Primeira Liga ta Portugal a wannan kakar.

    A wa’adinsa na farko a Real Madrid tsakanin 2010 zuwa 2013, Mourinho ya lashe La Liga, Copa del Rey da kuma Spanish Super Cup.

    Zai maye gurbin Alvaro Arbeloa, wanda aka naɗa a watan Janairu bayan tafiyar Xabi Alonso.

    Real Madrid ta kammala kakar 2025-26 ba tare da lashe kofi ba, yayin da abokiyar hamayyarta FC Barcelona ta ɗauki La Liga bayan nasarar 2-0 a El Clasico.

    Haka kuma tafiyar Real Madrid a Champions League ta kare bayan da Bayern Munich ta doke ta da jimillar 6-4 a zagayen quarter-final.

    Bayan da ya bar Real Madrid a 2013, Mourinho ya koma Chelsea karo na biyu, inda ya lashe kofin Premier League na uku a rayuwarsa da kuma EFL Cup a kakar 2014-15.

    Daga baya ya koma Manchester United a 2016, inda ya lashe Europa League, EFL Cup da Community Shield a kakarsa ta farko kafin a kore shi a 2018, saboda rashin sakamako mai kyau.

    Mourinho ya kuma horar da Tottenham da Roma — inda ya lashe Europa Conference League a 2022 — da kuma Fenerbahce kafin ya koma Benfica ta Portugal.

  2. Tripper zai koma Wolverhampton daga Newcastle, Premier League

    Wolverhampton Wanderers na dab da kammala yarjejeniya da tsohon ɗan wasan Ingila, Kieran Trippier.

    Ɗan wasan mai shekara 35 ya amince baki ɗaya ya koma Molineux a matsayin wanda bai da yarjejenia, bayan kare kwantiraginsa da Newcastle United.

    Ana sa ran zai sanya hannu kan kwantiragin shekara biyu tare da zaɓin ƙarin shekara guda, kuma zai zama farkon sayen koci Rob Edwards a bazarar nan.

    Trippier zai bar Newcastle bayan ya shafe shekara hudu da rabi a St James’ Park, inda ya buga wasa 160 ya kuma zura kwallo huɗu.

    Ya taimaka wa Newcastle wajen lashe EFL Cup a 2025, shi ne kofin gida da ta lashe na farko tun 1955.

    A baya, Trippier ya lashe La Liga tare da Atletico Madrid a 2020-21, sannan ya kai wasan karshe na UEFA Champions League a 2019 tare da Tottenham.

    Ya kuma buga wa Ingila wasa 54, inda ya ci ƙwallo a wasan kusa da na karshe a FIFA World Cup a 2018, sannan ya buga wasan karshe a UEFA Euro 2020 kafin ya yi ritaya daga buga wa ƙasarsa wasa a 2024.

  3. Volpato ya zaɓi buga wa Australia tamaula maimakon Italiya, Gasar kofin duniya

    Tsohon ɗan wasan Italiya ta matasa ƴan kasa da shekara 21, Cristian Volpato, ya yanke shawarar sauya wakilcin kasa daga Italiya zuwa Australia kafin a sanar da tawagar Australia domin gasar FIFA World Cup ta 2026 ranar 1 ga Yuni.

    Ɗan wasan tsakiya mai shekaru 22 an haife shi, ya kuma tashi ne a Sydney, amma yana da takardar zama ɗan kasa biyu bayan da ya koma Italiya a 2020 domin shiga makarantar matasan AS Roma.

    Daga baya ya koma ƙungiyar US Sassuolo Calcio a Serie A a shekarar 2023, kuma ya wakilci Italiya a matakin matasa.

    Saboda bai taba buga wa babbar tawagar Italiya wasa ba, Volpato yana cikin sharuddan da FIFA ta amince da su wajen bai wa ɗan wasa damar sauya kasa da zai wakilta a fannin taka leda.

    Yanzu an saka Volpato cikin tawagar farko ta Australia, kuma zai shiga sansanin horo a Los Angeles kafin koci Tony Popovic ya sanar da jerin ƴan wasa 26 a ranar Litinin.

  4. Messi zai buga wa Argentina gasar kofin duniya na shida jimila, Gasar kofin duniya

    Lionel Messi zai buga gasar FIFA World Cup ta shida a rayuwarsa bayan da aka saka shi cikin tawagar Argentina da za ta kare kofinta a gasar 2026.

    Ɗan wasan gaban, wanda zai cika shekara 39 a yayin gasar, ya kasance cikin jerin mutum 26 da koci, Lionel Scaloni ya fitar. Messi ne ya jagoranci Argentina zuwa lashe Kofin Duniya na uku a tarihinta a Qatar shekaru huɗu da suka gabata bayan doke Faransa a bugun fenariti.

    Da wasanni 26 da ya buga a Kofin Duniya, Messi ne ke rike da tarihin kan gaba a buga wasa a gasar. Zai kuma haɗu da Cristiano Ronaldo na Portugal a matsayin waɗandaa suka buga gasar sau shida a tarihi.

    Mai tsaron raga na Aston Villa, Emiliano Martinez, wanda aka zaɓa a matsayin mafi kyawun gola a gasar 2022, yana cikin tawagar. Haka kuma akwai Lisandro Martinez na Manchester United da Cristian Romero na Tottenham, duk da cewa Romero ya rasa karshen kakar Premier League saboda raunin gwiwa.

    Ƴan wasan tsakiya, Alexis Mac Allister na Liverpool da Enzo Fernandez na Chelsea su ma suna cikin ƴan wasa biyar da ke buga gasar Premier League ta Birtaniya da aka zaba domin gasar da za a yi a Amurka da Canada da kuma Mexico.

    Julian Alvarez na Atletico Madrid da Lautaro Martinez na Inter Milan suna cikin ƴan wasa 17 da suka lashe kofin 2022 da suka dawo domin kare kambun.

    Argentina tana rukuni na 10 kuma za ta fara gasar ne da Algeria a Kansas City ranar 17 ga watan Yuni, kafin ta kara da Austria a Dallas ranar 22 ga watan Yuni da kuma Jordan ranar 28 ga watan Yuni.

    Messi ya fita daga wasan Inter Miami a baya-bayan nan a MLS, amma ƙungiyar ta bayyana cewa bai samu rauni mai muni ba.

    Ya zuwa yanzu Messi ya buga wa Argentina wasa 198, wadda za ta yi karawar sada zumunta da Honduras a Texas da kuma Iceland a Alabama.

    Daga cikin manyan ƴan wasan da ba su samu gurbi ba akwai Emi Buendia na Aston Villa, wanda kwallonsa a wasan karshe na Europa League ta lashe ƙyautar mafi ƙyau a gasar, da Paulo Dybala na AS Roma wanda ya sha fama da jinya.

    Haka kuma matashin ɗan wasan Real Madrid mai shekara 18, Franco Mastantuono, bai samu gurbi ba.

    Dan wasan gefe na Benfica, Gianluca Prestianni, shi ma bai shiga ba bayan FIFA ta ce zai rasa wasanni biyu na farko saboda cin mutuncin Vinicius Junior.

    Jerin Ƴan wasan tawagar Argentina a gasar Kofin Duniya:

    Masu tsare raga: Juan Musso (Atletico Madrid), Geronimo Rulli (Marseille), Emiliano Martinez (Aston Villa).

    Masu tsare baya: Leonardo Balerdi (Marseille), Nicolas Tagliafico (Lyon), Gonzalo Montiel (River Plate), Lisandro Martinez (Manchester United), Cristian Romero (Tottenham), Nicolas Otamendi (Benfica), Facundo Medina (Marseille), Nahuel Molina (Atletico Madrid).

    Masu buga tsakiya: Leandro Paredes (River Plate), Rodrigo de Paul (Inter Miami), Valentin Barco (Strasbourg), Giovani lo Celso (Real Betis), Ezequiel Palacios (Bayer Leverkusen), Alexis Mac Allister (Liverpool), Enzo Fernandez (Chelsea).

    Masu cin ƙwallaye: Julian Alvarez (Atletico Madrid), Lionel Messi (Inter Miami), Nicolas Gonzalez (Atletico Madrid), Thiago Almada (Atletico Madrid), Giuliano Simeone (Atletico Madrid), Nico Paz (Como), Jose Manuel Lopez (Palmeiras), Lautaro Martinez (Inter Milan).

  5. Arsenal za ta tsawaita kwantiragin koci Arteta, Premier League

    Arsenal ta bayyana cewa babban abin da ta sa a gaba yanzu shi ne sabunta kwantiragin kocinta Mikel Arteta bayan da ya jagoranci ƙungiyar zuwa lashe kofin Premier League na farko cikin shekaru 22.

    Arteta, wanda a watan da ya gabata ya ce yana da cikakken kudurin ci gaba da zama a Emirates, yana da sauran shekara ɗaya a kwantiraginsa wanda zai kare a karshen kakar wasa mai zuwa.

    Shugaban Arsenal, Josh Kroenke, ya shaida wa kafafen yada labarai na Birtaniya cewa:

    “Labari mai dadi ga magoya bayan Arsenal a duniya shi ne yana jin dadin aikin da yake yi kuma yana son kasancewa a nan. Tun daga lokacin da yake ɗan wasa har zuwa yanzu, mutum ne na Arsenal gaba ɗaya.”

    Kroenke ya kuma yaba wa Arteta kan irin sauyin da ya kawo a ƙungiyar.

    “Idan akwai mutum guda da za a iya danganta wannan nasara da shi, zan bai wa Mikel, ma’aikatansa da ƴan wasa cikakken yabo,” in ji shi.

    Kakar Arsenal na iya kara zama ta tarihi idan ta doke Paris Saint-Germain a wasan karshe a UEFA Champions League ranar Asabar.

    Duk da cewa lashe gasar zakarun Turai a karon farko zai kara kuɗin shiga a Gunners, Kroenke ya ce ko menene sakamakon wasan karshe, Arsenal za ta kashe kuɗi domin kara karfafa ƙungiyar a kasuwar saye da sayar da ƴan wasa ta bazara.

  6. Bincike ya nuna magoya baya na son a ci gaba da VAR duk da matsalolinta, VAR

    Wani sabon bincike da kamfanin YouGov ya gudanar ya nuna cewa mafi yawan magoya bayan Premier League ba sa son a soke tsarin bidiyon VAR gaba ɗaya, duk da cewa da dama suna ganin har yanzu tsarin na aiki ne cikin matsalolo.

    An fara amfani da VAR a gasar Premier League tun kakar 2019-20, kuma har yanzu tana daga cikin batutuwan da ke jawo cece-kuce sosai a harkar ƙwallon kafa.

    Ƙwanan nan, ɗan siyasar Burtaniya, Andy Burnham ya bayyana cewa yana son a soke VAR gaba ɗaya daga wasan ƙwallon kafa.

    Sai dai binciken YouGov ya nuna cewa kaso 18 cikin 100 ne kacal daga cikin mutane 434 masu kallon wasannin Premier League akai-akai suka amince da wannan ra’ayi.

    Ra’ayin da ya fi karɓuwa shi ne a ci gaba da amfani da VAR amma tare da yin gyare-gyare kan yadda ake amfani da ita. Kashi 68 cikin 100 na waɗanda aka tambaya sun goyi bayan wannan matsayi, yayin da kaso 12 suka ce suna son a ci gaba da amfani da fasahar ba tare da wani sauyi ba.

    Duk da haka, mutane da dama har yanzu na kallon VAR a matsayin tsarin da bai yi aiki yadda ya kamata ba. Kashi 59 cikin 100 sun ce tsarin ya yi aiki cikin rashin gamsarwa, adadin da bai canza ba idan aka kwatanta da binciken YouGov da aka gudanar shekaru biyu da suka gabata.

    Haka kuma, kusan kashi uku cikin huɗu na masu kallon ƙwallon kafa akai-akai — wato kaso 72 cikin 100 — sun ce VAR ya rage musu dadin kallon wasanni.

  7. Ibrahima Konate zai bar Liverpool da zarar yarjejeniyarsa ta kare, Liverpool

    Ɗan wasan Liverpool, Ibrahima Konate, na dab da barin ƙungiyar, idan kwantiraginsa ya kare a watan Yuni.

    Rahotanni sun nuna cewa Konate da Liverpool za su raba gari ne saboda rashin daidaito tsakanin bangarorin biyu kan albashi da inganta sabuwar kwantiragi.

    Ɗan wasan mai shekara 27 ya koma Liverpool daga RB Leipzig a shekarar 2021 kan fam miliyan 35, inda ya sanya hannu kan yarjejeniyar shekaru biyar.

    Tun farko, bangarorin biyu suna son sabunta kwantiragin. A watan Afrilu bayan wasan Merseyside derby, Konate ya shaida wa manema labarai cewa sun “kusa cimma yarjejeniya” kuma akwai “babbar dama” da zai ci gaba da zama a Anfield a kakar wasa mai zuwa.

    An fara tattaunawa tun watan Nuwamban 2023, amma har yanzu ba a kai ga matsaya ba.

    Yanzu dai an fahimci cewa tattaunawar ta tsaya cik, kuma Konate zai iya zama sabon ɗan wasa mara kwantiragi da zai bar Liverpool a wannan bazarar bayan Andy Robertson da Mohamed Salah.

    A bara kuma, Trent Alexander-Arnold ya koma Real Madrid wata guda kafin kwantiraginsa ya kare, bayan da Madrid ta biya kudin sakin sa da wuri domin ya buga gasar Club World Cup.

    Kyaftin din Liverpool, Virgil van Dijk, shi ma kwantiraginsa zai kare a bazara mai zuwa, yayin da ƙungiyar ta kasa ɗaukar Marc Guehi a ranar karshe ta kasuwa a bara kafin daga baya ya koma Manchester City a watan Janairu.

  8. Arteta da Rice sun lashe kyautar koci da kuma ɗan wasa mafi hazaƙa a Premier, Kyautar BBC ta ƙarshen kaka

    Kocin Bournemouth Andoni Iraola ya samu ƙuri’u da dama a alokacin zaɓen, haka nan ma Keith Andrews na Brentfot da kuma kocin Sunderland Regis Le Bris – to amma dukkanin su babu wanda ya kamo Arteta – mutumin da ya kawo ƙarshen jira na shekara 22 ba tare da Arsenal lashe kofin gasar Premier ba.

    Mikel Arteta ya sanya Arsenal a saman teburin Premier tun daga watan Oktoba har ƙarshen kaka, kuma ya kai ƙungiyar zuwa wasan ƙarshe na gasar zakarun turai ta Champions League.

    A ɓangaren ɗan wasan da ya fi ƙwazo, ɗan wasan tsakiya da ya kitsa nasarar Arsenal har ta lashe kofi, Declan Rice shi ne ya ciri tuta.

    Rice ya ja ragamar Arsenal ta hanyar iya ɗauko bugun ƙusurwa da kuma zura ƙwallo ta kowane fanni har ta kai ga Arsenal ta lashe kofin Premier bayan kammalawa a matsayi na biyu sau uku a jere.

    Bruno Fernamndes na Manchester Unted wanda ya so yi wa Rice ƙafar ungulu wajen samun kyautar shi ne ya kafa tarihin taimakawa a ci ƙwallo a cikin kakar wasa ɗaya.

    Daga nan sai ɗan wasa Igor Thiago na Brentford ya zo matsayi na uku bayan jefa ƙwallo 22.

  9. Neymar ya samu rauni gab da fara Gasar Kofin Duniya

    Ɗan wasan gaba na Brazil Neymar Jr ba zai buga wasannin sada zumunta da tawagar ƙasarsa za ta yi a kwanan nan ba, kuma akwai yiwuwar zai iya rasa wasan farko da ƙasarsa za ta yi a Gasar Kofin Duniya.

    Yanzu an bayyana cewa ɗan wasan mai shekara 34 ba zai buga ƙwallo ba na tsawon mako biyu zuwa uku.

    Hakan na nufin ba zai buga wasan sada zumunta da ƙasarsa za ta yi da Panama ba a gida ranar Lahadi, da kuma wanda za ta yi da Masar a birnin Cleveland na Ohia a ranar Asabar ta sama.

    Brazil, wadda ta lashe kofin duniya sau biyar na cikin rukunin C na gasar kofin duniya kuma za ta yi wasanta na farko ne a ranar 13 ga watan Yuni inda za ta kara da Morocco a birnin New Jersey na Amurka.

    Daga nan za ta yi wasa na biyu da Haiti a Philadelphia ranar 19 ga watan Yuni, sai kuma karawarta da Scotland a Miami a ranar 24 ga watan Yuni.

    Likitan tawagar Brazil, Rodrigo Lamar ya sanar da raunin Neymar ne a wani taron manema labarai, inda ya ce: "An yi wa Neymar duk wasu gwaje-gwaje, inda a ƙarshe aka gano cewa ya samu rauni a tsokar bayan ƙafarsa. Ana sa ran zai warware nan da mako biyu ko uku".

    Neymar wanda ya ci wa Brazil ƙwallo 79 a wasa 128, ya tafi sansanin horaswar tawagar ne a ranar Talata sai dai bai samu yin atisaye ba a ranar Laraba, inda aka tura shi domin yin gwaje-gwaje bayan ganin wani kumburi a bayan ƙafarsa ta dama.

  10. Crystal Palace ta lashe kofin Conference League

    Ɗan wasa Jean-Philippe Mateta ne ya zura ƙwallon da ta bai wa Crystal Palace nasarar lashe kofin gasar nahiyar Turai na farko, inda ƙungiyar ta doke Rayo Vallecano da 1-0 a wasan ƙarshe na gasar Conference League.

    Dukkanin ƙungiyoyin biyu na fafutika ne ta lashe kofin farko a gasar nahiyar Turai.

    Crystal Palace ta samu shiga gaba ne a wasan a minti na 6 bayan dawowa daga hutun rabin lokaci.

    Wannan ce ƙwallo ta 16 da Mateta ya zura a raga a wannan kakar wasa - ɗan wasan da ƙiris ya rage ya bar ƙungiyar a watan Janairu in bacin rauni da ya hana tafiyarsa zuwa AC Milan.

    Rayo, ƙungiyar da ke buga gasar La Liga ta Spain ta gaza taɓuka abin kirki a wasan.

  11. , Daga Jaridu

    Tottenham ta sake nuna sha'awarta a kan cinikin dan wasan gaba na gefe na Manchester United Savinho, dan Brazil mai shekara 22, a kan fam miliyan 60. (Mail), external

    Liverpool ta fi son maye gurbin Mohamed Salah, da matashin dan wasan RB Leipzig, Yan Diomande, mai shekara 19, dan Ivory Coast, wanda kwantiraginsa ya tanadi damar sayar da shi a kan fam miliyan 86.

    Haka kuma daga cikin zabin da Liverpool din ke dubawa akwai dan wasan Newcastle da Ingila Anthony Gordon, mai shekara 25, da kuma dan gaban Paris St-Germain da Faransa Bradley Barcola, mai shekara 23. (Telegraph)

    Sai dai kuma suma zakarun gasar Jamus - Bundesliga - Bayern Munich suna son Gordon din na Newcastle, kuma Bayern za ta iya hadawa da mai tsaron ragar Jamus Alexander Nubel mai shekara 29, ta bayar a cinikin na Gordon. (Bild)

    Barcelona za ta yi sabuwar tattaunawa da Manchester United kafin wasan Kofin Duniya, domin kammala cinikin Marcus Rashford, inda kungiyar ta Sifaniya tauni ta kammala yarjejeniya tsakaninta da dan gaban na Ingila mai shekara 28 (Talksport)

  12. Kocin Sifaniya ya ce kishin ƙasa ya fi kowacce ƙungiya girma, Gasar kofin duniya

    Kocin Sifaniya, Luis de la Fuente, ya jaddada cewa kishin tawagar ƙasa ya fi na kowacce ƙungiya muhimmanci.

    Ya bayyana hakan bayan fitar da jerin ƴan wasan da za su buga wasa ksar FIFA World Cup ba tare da wani ɗan ƙwallon Real Madrid ba a ciki.

    Sifaniya, wacce ita ce zakarar kofin nahiyar Turai, na cikin manyan kasashen da ake ganin za su iya lashe gasar Kofin Duniya mai zuwa. Tawagar ƴan wasa 26 da De la Fuente ya zaba ta kunshi takwas daga Barcelona, abin da ya sake jawo cece-kuce kan hamayyar El Clasico zuwa cikin tawagar ƙasa.

    Masu tsaron baya Dean Huijsen da Dani Carvajal suna cikin fitattun ƴan wasan Real Madrid da aka bari daga tawagar da ke neman lashe kofin duniya na biyu bayan nasarar da ta samu a 2010 a Afirka ta Kudu.

    Sai dai De la Fuente ya yi watsi da ra’ayin cewa wannan hukunci zai rage masa goyon bayan magoya bayan Real Madrid.

    Ya bayyana cewa a wurinsa, abin da ya fi muhimmanci shi ne wakiltar Sifaniya yadda ya kamata, ba wai duba daga wace ƙungiya ɗan wasa ya fito ba.

  13. , Daga Jaridu

    Dan wasan tsakiya na Chelsea da Argentina Enzo Fernandez, mai shekara 25, ya zama wanda Manchester City ta fi son saye a kasuwar bazara. (Fichajes)

    Roma na sha'awar sayen dan wasan gaba na Marseille Mason Greenwood, mai shekara 24, da Joshua Zirkzee na Manchester United, dan Netherlands mai shekara 25, da kuma, Crysencio Summerville na West Ham, mai shekara 24 shi ma dan Netherlands, a shirin da kungiyar ta Italiya ke yi na tunkarar gasar Zakarun Turai mai zuwa.(La Gazzetta dello Sport )

    End of contentJulian Alvarez na son barin Atletico Madrid, kuma ana ganin Arsenal, za ta dage wajen ganin ta dauki dan wasan na gaba na Argentina mai shekara 26. (Teamtalk)

    Yayin da Aston Villa ke shirin tunkarar gasar Zakarun Turai ta kaka mai zuwa, tana sa ran sayen dan wasan gaba na gefe na Newcastle kuma dan Ingila Harvey Barnes, mai shekara 28. (Mail)

  14. Gundogan ya gargadi magoya baya kan kwatanta wani koci da Guardiola, Premier League

    Tsohon ƙyaftin ɗin Manchester City, Ilkay Gundogan, ya gargadi mutane da kada su rika kwatanta wanda zai maye gurbin Pep Guardiola da fitaccen kocin da ke barin ƙungiyar din.

    Guardiola ya yi bankwana da Manchester City a karshen mako bayan shekara 10 a filin Etihad inda ya lashe kofuna 20 tare da ƙungiyar.

    Tsohon kocin Chelsea, Enzo Maresca, wanda ya taba zama mataimakin Guardiola a kakar da City ta lashe uku a 2022-23, shi ne ake ganin zai fi kusa da maye gurbinsa.

    Gundogan, wanda ya jagoranci ƙungiyar lokacin da ta lashe kofi uku rigis, ya ce akwai sunaye da dama da ake dangantawa da aikin, kuma nan gaba za a san wanda zai zama sabon koci.

    Sai dai ya ce bai kamata a rika kwatanta sabon kocin kai tsaye da Guardiola ba.

    Ɗan wasan na Jamus ya bar Manchester City a bazarar bara kuma yanzu yana taka leda a Galatasaray.

  15. Bowen ya nemi afuwar magoya bayan West Ham bayan faduwa, Premier League

    Ƙyaftin ɗin West Ham United, Jarrod Bowen, ya nemi afuwar magoya baya, saboda “kunya da raɗaɗin” faduwa daga Premier League da ta jawowa ƙungiyar.

    Zaman shekara 14 da West Ham ta yi a gasar Premier League ya zo karshe a ranar Lahadi, duk da nasarar da suka samu da cin Leeds United 3-0. Sai dai nasarar ta zo ne a makare bayan mummunar kakar da ta hana su wuce Tottenham a teburi.

    Faɗuwar West Ham zuwa Championship ta zo shekara uku bayan ɗaya daga cikin manyan nasarorin da ta samu, lokacin da kwallon Bowen a Prague ta bai wa kungiyar nasara kan Fiorentina domin lashe kofin UEFA Europa Conference League.

    Bowen ya bayyana takaicinsa kan yadda kakar ta kare, yana mai cewa ƴan wasan sun fahimci irin zafin da magoya baya ke ciki bayan da ƙungiyar ta kasa tsira.

    A gefe guda kuma, ana sa ran koci Nuno Espirito Santo zai bar ƙungiyar a wannan makon bayan ganawa da shugabannin West Ham.

    Nuno ya karɓi aikin horar da ƙungiyar ne a watan Satumba lokacin da take matsayi na 19 a teburin Premier League, amma bai samu nasarar ceto ƙungiyar daga faduwa ba.

  16. , Daga Jaridu

    Juventus na dab da cimma yarjejeniya a cinikin mai tsaron ragar Liverpool da Brazil Alisson, wanda ke da ragowar sama da wata 12 a kwantiraginsa da Liverpool. (Goal Italia)

    Liverpool ta shiga gogayyar sayen matashin danwasan tsakiya na Jamus Kennet Eichhorn, mai shekara 16, daga Hertha Berlin. (Sky Germany)

    Bernardo Silva ya yi tattaunawa mai armashi da Atletico Madrid a yunkurin da kungiyar ta Sifaniya ke yi na yi wa Juventus shigar sauri a kan danwasan na tsakiya na Manchester City da Portugal, mai shekara 31, wanda zai tafi a matsayin wanda babu wani kwantiragi a kansa. (Teamtalk)

    Masu horad da 'yan wasa, Scott Parker, mai shekara 45, wanda a kwanan nan ya bar Burnley, da kuma na Strasbourg Gary O'Neil, mai shekara 43, dukkansu 'yan Ingila, na daga cikin wadanda West Ham, ke so idan ta rabu da kociyanta Nuno Espirito Santo, dan Portugal mai shekara 52, a bazaran nan. (Guardian)

    AC Milan ta tuntubi wakilan kociyan Bournemouth Andoni Iraola, dan Sifaniya mai shekara 43, bayan da kungiyar ta Italiya ta kori kociyanta Massimiliano Allegri mai shekara 58. (Sky Sports).

  17. Morgan Gibbs-White na ganin Ingila za ta lashe Kofin Duniya, Gasar kofin duniya

    Dan wasan Nottingham Forest, Morgan Gibbs-White, ya bayyana cewa yana da yakinin Ingila za ta iya lashe gasar FIFA World Cup, duk da bai samun gurbin wakiltar kasar ba.

    Gibbs-White, wanda ya buga wa Ingila wasa shida, yana cikin ƴan ƙwallon da koci Thomas Tuchel ya bari a jerin sunayen da aka fitar a makon da ya gabata.

    Duk da cewa an cire wasu fitattun ƴan wasa kamar Phil Foden da Cole Palmer saboda rashin gamsarwa a kakar bana, Gibbs-White ya zura kwallaye 15 a Premier League.

    Ɗan wasan mai shekara 26 ya ce yana jin ya yi duk abin da zai iya domin samun dama a tawagar, kuma yanzu yana bai wa waɗanda aka zaba cikakken goyon baya.

    Ya nuna cewa Ingila na da ingantattun ƴan wasa da zai su iya lashe Kofin Duniya, duk da takaicinsa na rashin kasancewa cikin tawagar.

  18. Portland Timbers ta raba gari da koci Neville, MLS

    Ƙungiyar Portland Timbers ta tabbatar da raba gari da kocinta, Phil Neville ta hanyar yarjejeniyar da aka cimma a tsakanin bangarori biyu.

    Wasan karshe da Neville ya jagoranta shi ne rashin nasara 3-1 da suka yi a hannun San Jose Earthquakes a ranar Lahadi, sakamakon da ya bar Timbers a matsayi na uku daga kasan teburi a Western Conference, maki takwas a baya da gurbin shiga play-offs na MLS kai tsaye.

    Neville, mai shekaru 49, ya gode wa ƙungiyar da duk waɗanda suka yi aiki tare da shi a Oregon, amma ya amince cewa bai cimma sakamakon da ake bukata ba a wannan kakar.

    Tsohon ɗan wasan Manchester United da tawagar Ingila ya koma Portland Timbers a 2023, watanni biyar bayan da aka kore shi daga Inter Miami.

    Kafin haka, ya taɓa horar da tawagar mata ta Ingila, inda ya jagorance su zuwa zagayen kusa da na karshe a gasar Kofin Duniya ta 2019.

  19. Nicky ya naɗa mahaifinsa mataimakinsa a Quuens of the South, Queens of the South

    Nicky Clark ya naɗa mahaifinsa mataimakinsa a lokacin da tsohon ɗan wasan Rangers da Dundee United zai fara aikin kociyan, Queens of the South.

    Ɗan wasan mai shekara 34 ya koma Palmerston Park a zagaye na biyu a kakar wasan da ta gabata, inda ya zura ƙwallaye bakwai a wasa 13 da ya buga.

    Zai ci gaba da taka leda a kakar wasa mai zuwa, yayin da ƙungiyar Queen of the South ta Scottish League One ke da kwarin gwiwar cewa suna da tsarin da zai ba shi damar hada aikin wasa da kuma horarwa a lokaci guda.

    Sandy, mai shekara 69, ya dawo a matsayin mataimakin koci na Queens karo na uku, bayan da ya taɓa aiki sau biyu a karkashin Allan Johnston a baya.

    A matsayinsa na tsohon ɗan wasan gaba a Rangers da Heart of Midlothian, ya bar aikin koci a ƙungiyar Albion Rovers ta Lowland League domin komawa aiki tare da dansa.

    A karo na karshe da suka yi aiki tare a Palmerston shi ne a kakar 2012–13, lokacin da suka lashe Second Division da Challenge Cup, inda Nicky Clark ya zura ƙwallaye 41 a wasanni 46.

  20. AC Milan ta kori kociyanta Massimiliano Allegri, Serie A

    AC Milan ta kori kocinta, Massimiliano Allegri bayan gazawar da ta yi wajen samun gurbin shiga gasar Champions League, a kakar da shugabancin ƙungiyar ya bayyana a matsayin “babban gazawa mai girma”.

    Milan ta faɗi daga matsayi na uku a teburin Serie A zuwa Ta biyar a Serie A, sakamakon shan kashi 2-1 a hannun Cagliari a wasan karshe na kakar ranar Lahadi, wanda ya sa ta rasa tikitin Champions League a karo na biyu a jere.

    A sakamakon haka, Inter Milan, Napoli, Roma da Como — wacce za ta fara shiga gasar a karon farko a tarihinta — za su wakilci Italiya a Champions League a baɗi, yayin da AC Milan tare da Juventus za su buga Europa League.

    Allegri mai shekara 58 ya dawo Milan ne a watan Mayun bara domin wa’adi na biyu, bayan da ya maye gurbin Sergio Conceição.

    A baya ya horar da Milan tsakanin 2010 zuwa 2014, inda ya lashe Serie A a kakar 2010–11 da kuma Super Cup na Italiya a kakar da ta biyo baya.

    Milan ta sha kashi a wasanni bakwai daga cikin 13 na karshe a kakar nan, yayin da abokiyar hamayya Inter Milan ta lashe Scudetto na biyu cikin shekaru uku.