Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Laraba 15/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Laraba 15/07/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Iran ta yi barazanar rufe hanyoyin fito na ƙawayen Amurka

    Dakarun juyin juya halin Iran sun yi barazanar rufe duka hanyoyin da ƙasashe ƙawayen Amurka ke fitar da kayyakinsu zuwa ƙetare a matsayin martani ga datse tasoshin ruwanta da Amurka ke yi.

    Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar sa'o'i bayan da Amurka ta sanar da datse tasoshin ruwan, ta ce za ta lalata hanyoyin fiton kayayyaki da ƙasashe ƙawayen Amurka ke amfani da su, idan aka ci gaba da toshe wa Iran hanyoyin fitar da manta.

    "Tun da aka datse wa Iran hanyoyin fitar da mai da iskar gas ɗinta domin durƙusar da tattalin arzikinmu, wadda ke zama barazana ga tattalin arzikin ƙawayen Amurka, to muma a jira namu matakin na datse hanyoyin fiton ƙasashen'', in ji sanarwar da IRGC.

  2. An yanke wa sojan Isra'ila hukuncin ɗaurin shekara biyar

    Rundunar sojan Isra'ila ta ce ta yanke wa wani sojanta hukuncin ɗaurin shekara biyar a gidan yari saboda samunsa da laifin aika wa wasu jami'an Iran bidiyon yadda sojojin Isra'ila ke kakkaɓo makaman linzami.

    Sojojin Isra'ilar sun ce sojan ya aika bidiyoyi guda biyu waɗanda ''aka biya shi kuɗin tura su'' a lokacin yaƙin kwana 12 tsakanin ƙasashen biyu.

    Haka kuma rundunar sojin Isra'ila ta ce ta same shi da wasu bidiyoyin d ya naɗa a biranen Isra'ila, waɗanda ya aika su ga jami'an na Iran.

    A lokacin yaƙin, Isra'ila ta hana ɗaukar bidiyon wasu keɓantattun wuraren da yaƙi ya lalata.

  3. Amurka na goyon bayan farfaɗo da bututun man Iraƙi da Siriya

    Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce tana goyon bayan ƙoƙarin da Iraƙi da Siriya ke yi na farfaɗo da wani bututun ɗanyen mai da ya haɗa ƙasashen biyu.

    Wannan na daga cikin jerin matakai da aka sanar a baya-bayan nan don rage tasirin matakin da Iran ta ɗauka na hana jirage ruwa ratsawa ta mashigin Hormuz.

    Wani jami'i ya ce kamfanonin mai na Amurka za su taka rawa wajen sabunta aikin bututun man fetur na Kirkuk-Baniyas, wanda ya kusan daina aiki gaba ɗaya tun bayan mamayar da Amurka ta yi wa Iraƙi a shekarar 2003.

    Shugaba Trump ya ce Iraki za ta iya taka muhimiyar rawa saboda tana da arzikin man fetur kuma za su kulla yarjejeniyoyi da dama da ita.

    Ana sa ran wannan bututun zai riƙa jigilar ɗanyen man fetur daga filayen man Iraki zuwa gaɓar tekun Bahar Rum da ke Siriya.

  4. Mashigar Hormuz za ta ci gaba da kasancewa a rufe - Iran

    Dakarun juyin juya halin Iran sun ce mashigin Hormuz zai ci gaba da kasancewa a rufe, har sai Amurka ta dakatar hare-haren da take kaiwa ƙasar , kwana guda bayan da sojojin Amurka suka sake toshe tashoshin jiragen ruwa na Iran.

    Dakarun sun yi gargaɗin cewa za su iya faɗaɗa hare-haren da suke kaiwa zuwa wasu hanyoyin fitar da man fetur zuwa ƙasashen waje.

    Ɓangarorin biyu sun sake musayar hare-hare cikin dare, inda kafafen yaɗa labaran Iran suka ce an kai farmaki kan cibiyoyin Amurka da ke Bahrain da Kuwait da Jordan.

    Sojojin Amurka sun ce sun shafe tsawon sa'a bakwai suna kai wa Iran hari .

    Yayin da yarjejeniyar tsagaita wuta ke rushewa, Shugaba Trump ya sake yin barazanar kai hare-hare kan tashoshin lantarki da gadoji a Iran idan ba ta koma teburin tattaunawa ba.

  5. Assalama alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a wannan shafi domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Kuna iya tafka muhawara a shafukanmu na sada zumunta da muhawara kan labaran da muke wallafawa.